Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Published: 4th, June 2025 GMT
Sanarwar tafiyar tasa ta biyo bayan ganawar da Inzaghi ya yi da jami’an Inter a ranar Talata, sanarwar da Inter Milan ta fitar ta ce Kulob din da Simone Inzaghi sun yanke shawarar rabuwa, “Wannan shi ne shawarar da aka dauka bisa yarjejeniyar juna”, shugaban Inter Giuseppe Marotta ya kara da cewa “Ina so in gode wa Simone Inzaghi saboda aikin da ya yi, ya matukar taka rawar gani a shekaru 4 da muka shafe muna aiki tare, don haka Inter Milan na yi mashi fatan alheri a duk inda zai samu kanshi a nan gaba”.
Inzaghi ya lashe gasar Seria A daya, Coppa Italia biyu da kuma Supercoppa Italia sau uku a lokacin da ya ke San Siro, sau biyu ya jagoranci Inter zuwa wasan karshe na gasar zakarun Turai amma Manchester City ta doke su da ci 1-0 a 2022-23 sannan suka sha kashi a hannun PSG da ci 5-0 a ranar Asabar din da ta gabata.
Sun kuma kasa cin kofin Seria A na 2024-25 bayan da Napoli ta basu maki daya kacal akan teburi, tafiyar Inzaghi na zuwa ne gabanin halartar Inter a gasar cin kofin duniya na kungiyoyin kwallon kafa na Fifa da aka fadada, wanda zai gudana a Amurka tsakanin 14 ga watan Yuni zuwa 13 ga Yuli.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
Kungiyar ta malaman musulumi ta fitar da fatawa da a ciki ta bukaci gwamnatoci da al’ummar musulmi da su yunkura cikin gaggawa domin kawo karshen killace yankin Gaza da aka yi, da kuma wajabcin kai musu abinci da magunguna.
Kungiyar malaman musulmin ta kuma bayyana abinda HKI take yi na killace mutanen Gaza fiye da miliyan biyu da haka su abinci da magani,musamman mata, yara da manya,wani babban laifi ne da ba shi da tamka a cikin tarihi, tana mai yin kira ga al’ummu da gwamnatoci da su motsa saboda su taimaki raunana.
Kwamitin fatawa da yake a karkashin wannan kungiyar ta malaman musulmi, ya dogara da ayoyin alkrur’ani da hadisan ma’aiki ( s.a.w) da manufofi na shari’a da ka’idoji na fikihu da su ka wajabta taimakawa wadanda aka zalunta da kawar da zaluncin da ake yi masa.
Fatawar ta kuma bayyana cewa, kin taimakawa wajen taimakawa alhali da akwai dama, yana daidai da yin tarayyar a cikin laifukan yaki.
A wani gefen, bayanin da ya fito daga kungiyar malaman musulmin ya kuma yi kira ga al’ummu da su fito domin yin zanga-zanga da zaman dirshan a gaban ofisoshin jakadancin kasashen Amurka da turai.
Har ila yau fatawar ta bukaci kasar Masar da ta dauki nauyin da ya rataya a wuyanta na tarihi da addini, ta bude mashigar Rafaha, saboda a shigar da kayan abinci da dukkanin bukatun yau da kullum. Har ila yau ta ce, yin shiru akan wannan batun shi ne;yin shiru akan wannan bala’in bai dace da ma’abota ilimi da addini.”
Wani bangare na sakon kungiyar ta malaman musulunci ya shafi yin kira ga ma’abota tunani da alkalami da su rika aikewa da sakwanni ta shafukansu domin yin matsyin lamba saboda a kawo karsehn wannan bala’in da yake faruwa a Gaza.