Aminiya:
2025-07-24@03:41:12 GMT

Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga

Published: 3rd, June 2025 GMT

’Yan bindiga sun sako wani magidanci da suka yi garkuwa da shi da amaryarsa na tsawon wata bakwai, bayan sun bindige matar tasa tare da karɓar kuɗin fansa Naira miliyan 30 daga iyalansa.

A watan Oktobar 2024 ne ’yan bindiga suka yi garkuwa da mutumin suna Yakubu Dada tare da amaryarsa, a yayin da ma’auratan ke tafiya a kan babban titin zuwa Kontagora a Jihar Neja.

A lokacin ’yan bindigar sun buƙaci kuɗin fansa Naira miliyan 10 daga iyalan mutumin, wanda tsohon ma’aikacin gwamnati ne.

Ba su sako shi ba sai a ranar Litinin, bayan da suka karɓi ƙarin Naira miliyan 20 daga iyalansa, jimilla Naira miliyan 30 ke nan.

A lokacin da suka yi garkuwa da ma’auratan sun buƙaci Naira miliyan 10, amma bayan iyalansa sun yi karo-karo sun biya, sai ’yan ta’addan suka nemi ƙarin Naira miliyan 20 da sababbin babura ƙirar Bajaj, sa’nnna suka yi barazanar kashe ma’auratan idan ba a ba su ba.

A farkon watan Mayu 2025, suka bindige amaryar tasa mai suna Lami, a ƙoƙarinsu na matsa wa iyalan su biya musu buƙata.

Uwar gidarsa mai suna Maimuna, ta tabbatar wa Aminiya cewa an sake shi a wani daji da ke kusa da yankin Kotonkoro a Ƙaramar Hukumar Mariga ta Jihar Neja, bayan da iyalan suka biya ƙarin Naira miliyan 20.

Malama Maimuna ta bayyana farin cikinsu, amma ta ce Malam Yakubu bai riga ya ya iso gida ba a lokacin.

Ta bayyana cewa a watan Nuwambar 2024 sai da suka sayar da kusan duk abin da suka mallaka domin haɗa Naira miliyan 10 da aka buƙata, wanda ƙanin mijin nasu ya kai wa ’yan bindigar a wani daji a Jihar Kebbi.

Ta ce bayan nan ne ’yan ta’ddan suka nemi ƙarin Naira miliyan 60 amma daga ƙarshe aka daidaita da su a kan Naira miliyan 20 da sababbin babura guda huɗu, buƙatar a iyalan suka yi ƙoƙarin biya kafin a sako shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Garkuwa Kontagora ƙarin Naira miliyan Naira miliyan 20

এছাড়াও পড়ুন:

A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da a tsananta hukunci kan masu cin zarafin ’ya’ya mata, yana mai cewa babu wani musulmi nagari da zai yi wa matarsa dukan da har zai yi mata lahani.

A yayin da yake tunatar da malamai da limamai kan muhimmiyar gudunmawar da za su bayar a wannan fage domin yi wa tufkar hanci, Sarkin ya bayyana damuwa kan yadda matsalolin fyade da kuma samun magidantan da ke dukan matansu suka zama ruwan dare a Jihar Kano.

Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRC Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh

Sarki Sanusi na wannan furuci yayin da ya karbi bakuncin tawagar cibiyar bunkasa bincike (dRPC) da kuma cibiyar nazarin addinin musulunci ta Jami’ar Bayero da ke Kano (CCID) suka kai ziyara fadarsa ta Gidan Rumfa a birnin Dabo.

A cewar Sarkin, “ban zan taba goyon dukan mace ba, kuma duk masu yi, suna yi ba da niyyar ladabtarwa ba. Amma abin takaicin da muke gani a yau shi ne yadda ake yi wa mata jina-jina da sunan ladabtarwa.

“Musulunci yana fifita mata da daraja fiye da kowane addini kuma duk masu neman fakewa a karkashinsa don cin zarafinsu, ba su ma fahimci addinin ba.

“Duk wanda yake dukan matarsa har ya yi mata rauni ba mutumin kirki ba ne, kuma ba ni na fadi haka ba, Annabi Muhammad (SAW) ne ya fada, wadanda ba su karanta ba ne ba su sani ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
  • Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare
  • An Kama Wata Mata Da Take Shirin Kashe Benjemin Netanyahu
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
  • Hisbah Ta Lalata Barasa Ta Naira Miliyan 5.8 A Jigawa
  • A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
  • Gwamna Radda Da Makarrabansa Na Samun Kulawa A Asibiti Bayan Hatsarin Mota A Hanyar Daura