Masu sayar da rago a jihar Zamfara sun nuna damuwarsu kan rashin samun ciniki gabanin bikin Eid-el-Kabir, duk da cewa ana samun dabbobi a kasuwanni.

 

Shugaban kungiyar masu sayar da dabbobi ta jihar Zamfara, Malam Saidu Ibrahim Gusau ya bayyana haka a wata tattaunawa da gidan rediyon Najeriya a Gusau.

 

Malam Gusau ya bayyana cewa, duk da cewa ana samun raguna da yawa, amma an samu karancin masu saye.

 

Sai dai ya bayyana fatan cewa lamarin zai iya gyaruwa yayin da bukukuwan Sallah ke kara gabatowa.

 

“Amma idan abubuwa sun ci gaba da haka, to gaskiya, akwai matsala ta gaske,”

 

“Har yanzu, na yi imani cewa da sauran kwanaki abubuwa za su iya canzawa, in sha Allah.”

 

Malam Saidu Gusau ya bayyana cewa, kungiyar ta yi kokarin ganin an samu rago musamman saboda kalubalen da ke tattare da rufe iyakokin kasar ta Jamhuriyar Nijar.

 

“Lokacin da shugaban kasar Nijar ya bayar da umarnin rufe iyakokin, hakan na nufin ba za a iya fitar da raguna zuwa wasu kasashen Afirka ba, shi ya sa muka yi nisa wajen ganin an shigo da raguna a cikin Zamfara domin jama’a su yi Sallar Idi cikin sauki.”

 

Shugaban ya koka da karin farashin kananan raguna idan aka kwatanta da shekarun baya.

 

“A shekarar da ta gabata, an sayar da mafi kankantar ragon da ya dace da hadaya a kan kudi kusan #40,000, amma a bana, ko da mafi kankantar farashinsa ya haura ₦100,000.”

 

“Yanzu awaki suna farawa daga ₦55,000 zuwa ₦60,000 zuwa sama, yayin da raguna mafi arha ke kan ₦70,000.”

 

Ya bayyana cewa, a karon farko a tarihin kasuwar dabbobi ta Gusau, an sayar da rago sama da Naira miliyan 1 a bana.

 

“A da, muna kai irin wadannan raguna masu kima ne kawai zuwa wasu kasuwanni inda masu siya za su iya sayen su, amma a bana, mun sayar da guda daya a kasuwarmu.”

 

Malam Saidu Ibrahim Gusau ya kuma yi kira ga ’yan uwansu masu sayar da raguna da su rika gudanar da sana’arsu da ikhlasi da tsoron Allah domin samun albarkar Ubangiji.

 

Wani mazaunin garin Gusau da ya isa kasuwar domin siyan rago da naira 50,000 ya nuna damuwar rashin samun haka.

 

Ya shaida wa wakilin gidan rediyon Najeriya cewa ya canja ra’ayinsa na sayen zai yi amfani da kudin ya sayi masara ga iyalansa.

 

Wani mai siyan rago a kasuwar ya ce abin da yake sa ran a duk shekara shi ne, za a iya kara farashin raguna, ya kuma shawarci kowa da ya rika kula da dabbar da zai iya samu.

 

 

 

COV/AMINU DALHATU.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Raguna Zamfara masu sayar da

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama

Babban Hafsan Hafsoshin Sojan Iran ya jaddada cewa: Idan makiya suka sake yin kuskure, za su fuskanci mayar da martani da karfi

Babban hafsan hafsoshin sojan kasar Iran Manjo Janar Abdulrahim Mousavi ya jaddada cewa: Idan makiya suka sake yin wani kuskure, to za su fuskanci mayar da martani mai karfi da zai wurga su cikin nadama kuma martini mai gauni ne fiye da na baya.

A yayin ganawarsa da gungun mayakan sojojin sama, Manjo Janar Mousavi ya mika sakon jinjina ga shahidan daukaka da karfin Jamhuriyar Musulunci musamman shahidi Major Janar Hajizadeh. Ya yaba da rawar da ya taka wajen ciyar da shirye-shiryen rundunar Sojan sararin samaniya da bunkasa karfin makamai masu linzami da jirage  marasa matuki ciki na kasar, ya kuma yi la’akari da kokarinsa a matsayin mai karfi da zaburarwa ga al’ummomi masu zuwa kuma masu dauke da ruhin kare kasarsu.

Mousavi ya bayyana rundunar Dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta IRGC a matsayin rundunar da ke haifar da alfahari da mutuntawa, yana mai cewa, “Bayyana wannan karfin da sojojin sararin samaniya suka gwada a lokacin yakin kwanaki 12 da aka kakaba wa Iran ya zarce duk abin da aka tsammata, kuma girman kokari da suka nuna ya fi muhimmanci fiye da manyan ayyukan da aka yi a lokacin tsaro mai alfarma.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Kano Za Ta Hada Gwiwa FMBN Don Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi
  • Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba
  • Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama
  • Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
  • A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi
  • Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye