Masu sayar da rago a jihar Zamfara sun nuna damuwarsu kan rashin samun ciniki gabanin bikin Eid-el-Kabir, duk da cewa ana samun dabbobi a kasuwanni.

 

Shugaban kungiyar masu sayar da dabbobi ta jihar Zamfara, Malam Saidu Ibrahim Gusau ya bayyana haka a wata tattaunawa da gidan rediyon Najeriya a Gusau.

 

Malam Gusau ya bayyana cewa, duk da cewa ana samun raguna da yawa, amma an samu karancin masu saye.

 

Sai dai ya bayyana fatan cewa lamarin zai iya gyaruwa yayin da bukukuwan Sallah ke kara gabatowa.

 

“Amma idan abubuwa sun ci gaba da haka, to gaskiya, akwai matsala ta gaske,”

 

“Har yanzu, na yi imani cewa da sauran kwanaki abubuwa za su iya canzawa, in sha Allah.”

 

Malam Saidu Gusau ya bayyana cewa, kungiyar ta yi kokarin ganin an samu rago musamman saboda kalubalen da ke tattare da rufe iyakokin kasar ta Jamhuriyar Nijar.

 

“Lokacin da shugaban kasar Nijar ya bayar da umarnin rufe iyakokin, hakan na nufin ba za a iya fitar da raguna zuwa wasu kasashen Afirka ba, shi ya sa muka yi nisa wajen ganin an shigo da raguna a cikin Zamfara domin jama’a su yi Sallar Idi cikin sauki.”

 

Shugaban ya koka da karin farashin kananan raguna idan aka kwatanta da shekarun baya.

 

“A shekarar da ta gabata, an sayar da mafi kankantar ragon da ya dace da hadaya a kan kudi kusan #40,000, amma a bana, ko da mafi kankantar farashinsa ya haura ₦100,000.”

 

“Yanzu awaki suna farawa daga ₦55,000 zuwa ₦60,000 zuwa sama, yayin da raguna mafi arha ke kan ₦70,000.”

 

Ya bayyana cewa, a karon farko a tarihin kasuwar dabbobi ta Gusau, an sayar da rago sama da Naira miliyan 1 a bana.

 

“A da, muna kai irin wadannan raguna masu kima ne kawai zuwa wasu kasuwanni inda masu siya za su iya sayen su, amma a bana, mun sayar da guda daya a kasuwarmu.”

 

Malam Saidu Ibrahim Gusau ya kuma yi kira ga ’yan uwansu masu sayar da raguna da su rika gudanar da sana’arsu da ikhlasi da tsoron Allah domin samun albarkar Ubangiji.

 

Wani mazaunin garin Gusau da ya isa kasuwar domin siyan rago da naira 50,000 ya nuna damuwar rashin samun haka.

 

Ya shaida wa wakilin gidan rediyon Najeriya cewa ya canja ra’ayinsa na sayen zai yi amfani da kudin ya sayi masara ga iyalansa.

 

Wani mai siyan rago a kasuwar ya ce abin da yake sa ran a duk shekara shi ne, za a iya kara farashin raguna, ya kuma shawarci kowa da ya rika kula da dabbar da zai iya samu.

 

 

 

COV/AMINU DALHATU.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Raguna Zamfara masu sayar da

এছাড়াও পড়ুন:

Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne

Wani yaro ɗan shekara 15 ya rasa ransa bayan mahaifinsa ya harbe shi bisa kuskure, yana zaton biri ne.

Wannan lamari mai ban tausayi ya faru ne a gonar magidancin inda shi da ɗan nasa suke aiki, a yankin Iye Ekiti da ke Ƙaramar Hukumar Ilejemeje ta Jihar Ekiti.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Ekiti,  Joseph Eribo, ya tabbatar da faruwar lamarin a yau a Ado-Ekiti.

Ya bayyana cewa manomin ya daɗe yana fama da hare-haren birai a gonarsa kuma ya kai bindiga domin kare amfanin gonarsa.

Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara An lakaɗa wa Mataimakin Firinsifal duka saboda hana satar a jarabawa

Binciken farko ya nuna cewa mahaifin ya lura da motsi a wata bishiya da ke kusa da shi, sai ya harba bindiga yana zaton biri ne. Bayan ya yi harbin sai ya gano cewa ya harbi dansa da ke kan bishiyar har lahira.

Tuni dai ’yan sanda suka tsare mahaifin domin yi masa tambayoyi yayin da bincike ke ci gaba kan wannan lamari mai ban tausayi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sallah: ’Yan sanda sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a Gombe
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Kano Ta Haramta Bukukuwan Hawan Sallah A Kano
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Bill Gates Da Lambar Girmamawa Ta CFR
  • Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa
  • Ana samun Karancin Masu Sayen Dabbobi A Kano Duk Karatowar Sallar Layya
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wani Gungun Masu Satar Motoci A Kwara
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hari kan Falasdinawa Masu Karban Agajin Jin Kai A Rafah
  • Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne