Masu sayar da rago a jihar Zamfara sun nuna damuwarsu kan rashin samun ciniki gabanin bikin Eid-el-Kabir, duk da cewa ana samun dabbobi a kasuwanni.

 

Shugaban kungiyar masu sayar da dabbobi ta jihar Zamfara, Malam Saidu Ibrahim Gusau ya bayyana haka a wata tattaunawa da gidan rediyon Najeriya a Gusau.

 

Malam Gusau ya bayyana cewa, duk da cewa ana samun raguna da yawa, amma an samu karancin masu saye.

 

Sai dai ya bayyana fatan cewa lamarin zai iya gyaruwa yayin da bukukuwan Sallah ke kara gabatowa.

 

“Amma idan abubuwa sun ci gaba da haka, to gaskiya, akwai matsala ta gaske,”

 

“Har yanzu, na yi imani cewa da sauran kwanaki abubuwa za su iya canzawa, in sha Allah.”

 

Malam Saidu Gusau ya bayyana cewa, kungiyar ta yi kokarin ganin an samu rago musamman saboda kalubalen da ke tattare da rufe iyakokin kasar ta Jamhuriyar Nijar.

 

“Lokacin da shugaban kasar Nijar ya bayar da umarnin rufe iyakokin, hakan na nufin ba za a iya fitar da raguna zuwa wasu kasashen Afirka ba, shi ya sa muka yi nisa wajen ganin an shigo da raguna a cikin Zamfara domin jama’a su yi Sallar Idi cikin sauki.”

 

Shugaban ya koka da karin farashin kananan raguna idan aka kwatanta da shekarun baya.

 

“A shekarar da ta gabata, an sayar da mafi kankantar ragon da ya dace da hadaya a kan kudi kusan #40,000, amma a bana, ko da mafi kankantar farashinsa ya haura ₦100,000.”

 

“Yanzu awaki suna farawa daga ₦55,000 zuwa ₦60,000 zuwa sama, yayin da raguna mafi arha ke kan ₦70,000.”

 

Ya bayyana cewa, a karon farko a tarihin kasuwar dabbobi ta Gusau, an sayar da rago sama da Naira miliyan 1 a bana.

 

“A da, muna kai irin wadannan raguna masu kima ne kawai zuwa wasu kasuwanni inda masu siya za su iya sayen su, amma a bana, mun sayar da guda daya a kasuwarmu.”

 

Malam Saidu Ibrahim Gusau ya kuma yi kira ga ’yan uwansu masu sayar da raguna da su rika gudanar da sana’arsu da ikhlasi da tsoron Allah domin samun albarkar Ubangiji.

 

Wani mazaunin garin Gusau da ya isa kasuwar domin siyan rago da naira 50,000 ya nuna damuwar rashin samun haka.

 

Ya shaida wa wakilin gidan rediyon Najeriya cewa ya canja ra’ayinsa na sayen zai yi amfani da kudin ya sayi masara ga iyalansa.

 

Wani mai siyan rago a kasuwar ya ce abin da yake sa ran a duk shekara shi ne, za a iya kara farashin raguna, ya kuma shawarci kowa da ya rika kula da dabbar da zai iya samu.

 

 

 

COV/AMINU DALHATU.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Raguna Zamfara masu sayar da

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

A cewar Salahudeen, Ranar Yaƙi da Cutar Polio ta Duniya muhimmiyar dama ce ta faɗakar da jama’a kan barazanar da cutar shan-inna ke haifarwa ga rayuwar al’umma da tattalin arziki, tare da sake duba nasarori da kalubalen da ake fuskanta.

 

Ya ce haɗin kai tsakanin gwamnatin jihar da kungiyoyin bunkasa lafiya — musamman Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) — ya taimaka matuƙa wajen cimma wannan gagarumar nasara.

 

“Gwamna Dauda Lawal ya ayyana dokar ta-baci a bangaren lafiya, kuma hakan ya zame ginshiqin da ya taimaka wajen samun tallafi, goyon baya da isassun ma’aikata don tabbatar da an kai rigakafi ko’ina,” inji shi.

 

Dekta Salahudeen ya kara da cewa WHO, UNICEF, Chigari, Sultan Foundation da Salina Foundation sun taka rawar gani wajen taimakawa jihar ta isa ga dukkan al’ummomi, ciki har da yankunan da ke da wahalar kaiwa.

 

Ya ce, waɗannan ƙungiyoyi sun samar da tallafin kudi, kayan aiki, horo ga ma’aikatan lafiya, da kuma goyon baya wajen aiwatar da rigakafi a kananan hukumomi 14 na jihar.

 

Daga cikin manyan nasarorin da aka samu, a cewar shi, akwai damar kai rigakafi har ma zuwa yankunan Fulani makiyaya da wuraren da ake gani a matsayin “hard-to-reach”, baya ga tallafin jami’an tsaro da ya taimaka wajen baje kolin ayyukan rigakafi cikin kwanciyar hankali.

 

“An samu damar ziyarar dukkan yankuna, har da na noma da kiwo, inda muka ga cewa ba zai yuwu mu bar kowane yaro a baya ba,” inji Salahudeen.

 

Ya ce gwamnatin jihar za ta ci gaba da hada karfi da kungiyoyin hadaka, domin tabbatar da kawar da shan-inna baki daya, tare da cigaba da karfafa wayar da kan jama’a kan muhimmancin rigakafi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara  October 30, 2025 Labarai Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai October 30, 2025 Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara