Masu Sayar da Rago Sun Koka A Zamfara Saboda Karancin Masaya
Published: 3rd, June 2025 GMT
Masu sayar da rago a jihar Zamfara sun nuna damuwarsu kan rashin samun ciniki gabanin bikin Eid-el-Kabir, duk da cewa ana samun dabbobi a kasuwanni.
Shugaban kungiyar masu sayar da dabbobi ta jihar Zamfara, Malam Saidu Ibrahim Gusau ya bayyana haka a wata tattaunawa da gidan rediyon Najeriya a Gusau.
Malam Gusau ya bayyana cewa, duk da cewa ana samun raguna da yawa, amma an samu karancin masu saye.
Sai dai ya bayyana fatan cewa lamarin zai iya gyaruwa yayin da bukukuwan Sallah ke kara gabatowa.
“Amma idan abubuwa sun ci gaba da haka, to gaskiya, akwai matsala ta gaske,”
“Har yanzu, na yi imani cewa da sauran kwanaki abubuwa za su iya canzawa, in sha Allah.”
Malam Saidu Gusau ya bayyana cewa, kungiyar ta yi kokarin ganin an samu rago musamman saboda kalubalen da ke tattare da rufe iyakokin kasar ta Jamhuriyar Nijar.
“Lokacin da shugaban kasar Nijar ya bayar da umarnin rufe iyakokin, hakan na nufin ba za a iya fitar da raguna zuwa wasu kasashen Afirka ba, shi ya sa muka yi nisa wajen ganin an shigo da raguna a cikin Zamfara domin jama’a su yi Sallar Idi cikin sauki.”
Shugaban ya koka da karin farashin kananan raguna idan aka kwatanta da shekarun baya.
“A shekarar da ta gabata, an sayar da mafi kankantar ragon da ya dace da hadaya a kan kudi kusan #40,000, amma a bana, ko da mafi kankantar farashinsa ya haura ₦100,000.”
“Yanzu awaki suna farawa daga ₦55,000 zuwa ₦60,000 zuwa sama, yayin da raguna mafi arha ke kan ₦70,000.”
Ya bayyana cewa, a karon farko a tarihin kasuwar dabbobi ta Gusau, an sayar da rago sama da Naira miliyan 1 a bana.
“A da, muna kai irin wadannan raguna masu kima ne kawai zuwa wasu kasuwanni inda masu siya za su iya sayen su, amma a bana, mun sayar da guda daya a kasuwarmu.”
Malam Saidu Ibrahim Gusau ya kuma yi kira ga ’yan uwansu masu sayar da raguna da su rika gudanar da sana’arsu da ikhlasi da tsoron Allah domin samun albarkar Ubangiji.
Wani mazaunin garin Gusau da ya isa kasuwar domin siyan rago da naira 50,000 ya nuna damuwar rashin samun haka.
Ya shaida wa wakilin gidan rediyon Najeriya cewa ya canja ra’ayinsa na sayen zai yi amfani da kudin ya sayi masara ga iyalansa.
Wani mai siyan rago a kasuwar ya ce abin da yake sa ran a duk shekara shi ne, za a iya kara farashin raguna, ya kuma shawarci kowa da ya rika kula da dabbar da zai iya samu.
COV/AMINU DALHATU.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Raguna Zamfara masu sayar da
এছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.
An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.
Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.
An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.
Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.
Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp