Babbar Sallah: Farashin kayan miya ya yi tashin gwauron zabo
Published: 3rd, June 2025 GMT
Farashin kayan miya, musamman kayan gwari ya yi tashin gwauron zabo a yayin da Babbar Sallah ta bana ta kawo jiki.
Kuɗin kayan lambu ya ninka sau uku a cikin mako biyu, a yayin da Babbar Sallar ta zo wa iyalai da dama a Najeriya a hagunce, a sakamakon fama da matsananciyar matsalar tsadar rayuwa.
Wannan hauhawan farashin, wana ta zarce abin da aka saba gani a lokutan rani, ya kasaara ƙarfin iyalai yin sayayya domin girki abincin Sallah, wanda hakan ya haifar da damuwa, musamman a jihohin Kano, Taraba, Kwara, da Jigawa.
Al’umma a Jihar Kano sun koka bisa mummunan tasirin wannan tsadar rayuwa. Wani ma’aikacin gwamnati mai ’ya’ya biyar, Malam Idris Bako, ya nuna damuwarsa.
NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindigaMalam Idris ya bayyana cewa, a baya a irin wannan lokaci an saba ganin kayan lambu sun yi arha, magidanta sun fi mayar ba da fifiko ga batun dabbar layya.
Ya ce amma a bana lamarin ya juya, “ma’ikata ba sa lissafin sayen abin layya saboda tsadar dabbobi. Abin takaici, mun yanke shawarar yin abinci mai kyau da sallah kuma mu jira baɗi, amma halin da ake ciki a yanzu ya kawo mana babbar damuwa.
“Kayan lambun da muke shirin saya don miyan Sallah suna neman fin da ƙarfinmu. Ƙwandon tumatir da ake sayarwa N12,000 a makon jiya, yanzu ya kai N35,000,” in ji shi.
Wata mata da ke zaune a unguwar Ja’oji, Malama Halima Bello, ta bayyana halin da ake ciki a matsayin mafi tsanani sa ta taɓa gani a shekaru talatin da suka gabata.
Ta nuna cewa iyalai da yawa sun watsar da shirinsu na yin layya saboda tsadar dabbobi, ga shi kuma yin miya mai kyau da Sallah ma na neman ta gagara.
Malama Hakima ta ce “Kwandon attarugu yanzu N40,000 yake, saɓanin N25,000 da aka sayar a wancan makon. Yana da matuƙar wahala ga iyalai yanzu su yi girkin Sallah yadda suka tsara d farko.”
A ziyarar da muka kai kasuwar kayan lambu ta ’Yan Kaba, mun lura cewa akwai matsakaicin wadatar kayan gwari, amma kuma babu masu zuwa saye sosai.
Farashin kwandon tumatir, wanda aka sayar da shi N11,000 zuwa N13,000 a makon da ya gabata, yanzu ya koma tsakanin N28,000 zuwa N35,000. Haka kuma, ana sayar da kwandon barkono kusan N43,000.
Mansur Simon, wani mai sayar da tumatir a Kasuwar ’Yankaba, ya danganta hauhawar farashin kayan da ƙaruwar buƙatun jama’a a lokacin sallah, yana mai cewa an saba ganin hakan.
Farashi ya ninku sau 3 a mako 2Haka lamarin yake a kasuwannin Jihar Taraba, inda farashin kayan lambu ya yi irin wannan tashin gwauron zabo.
A babbar kasuwar kayan lambu ta Jalingo farashin barkono, albasa, barkono, tumatir, karas, da kabeji sun ninka har sau uku a cikin makonni biyu.
Babban kwandon sabon tumatir, wanda aka sayar N8,000 watanni biyu da suka gabata, ya koma N35,000 zuwa N40,000. Buhun barkono mai nauyin kilo 100, wanda a da N35,000 ne, yanzu ya koma N110,000.
Attarugu ya haura daga N40,000 zuwa N130,000, yayin da barkono mai yaji na Habasha, wani nau’i na musamman na yankin, ya haura daga N50,000 zuwa N160,000-N170,000.
Hatta busasshen barkono da albasa su ma sun yi irin wannan tashin gwauron zabo.
Muhammed Tukur, wani dillalin kayan lambu, ya bayyana cewa kayan sun ƙare a wuraren da ake kawo su daga jihohin Gombe, Bauchi, Zariya, da Yobe, kuma a halin yanzu ba a yi girbin na damina ba.
Ƙorafi a Kasuwar ShuwarinA Jihar Jigawa, a Kasuwar Shuwarin, Malam Isah Aƙilu, mai sayar da tumatir da barkono, ya bayyana yadda farashin ya ninka.
Buhun attarugu ya koma yanzu N125,000 zuwa N150,000, kwandon tumatir yana tsakanin N30,000 zuwa N40,000, buhun albasa kuma N25,000.
Malam Aƙilu ya bayyana cewa suna yawan samun ƙorafi daga abokan ciniki game da tashin gwauron zabon kayan lambu a kasuwar.
Ƙarin kashi 10 a KwaraJihar Kwara ma an samu tsadar tumatir. Bincike a kasuwanni a Ilorin ya nuna ƙaruwar farashin tumatir kashi 10 cikin 100, idan aka kwatanta da farashin makonni biyu baya.
Yanzu kwandon tumatir ya kai tsakanin N18,000 zuwa N70,000, ya danganci girma da ingancin kayan.
Wata ’yar kasuwa a Ilorin, Iya Aisha Alata, ta tabbatar da cewa kwandon da aka sayar N40,000 a makon jiya yanzu N50,000 ne.
Wata matar aure, Madam Nice Oladuni ta nuna damuwarta ganin yadda farashin ƙaramin kwandon da ta saya N2,500 a makon da ya wuce ya ninka zuwa N5,000 a ranar Lahadi.
Dalilin tsadar kayan miyaDuk da yake wasu suna danganta hauhawar farashin da bukukuwan Babbar Sallah, wasu kuma na ganin ambaliyar ruwa da aka yi kwanan nan a Jihar Neja, wadda ta kawo cikas ga sufuri ga jigilar kayayyaki, shi ne sababi.
Iya Aisha ta bayyana kyakkyawan fata cewa farashin na iya daidaita bayan Sallah, tana mai danganta hauhawar farashin da yanayi da bukukuwan Sallah.
Har ila yau, ta lura da sauye-sauyen hanyoyin samar da kayayyaki daga tumatirin Hausawa zuwa waɗanda ke fitowa daga Kudu maso Yamma, wanda ke ba da gudummawa ga bambancin farashi.
Ra’ayoyin ƙwararru kan tsadar kayan lambuAlhaji Sani Yadakwari, Shugaban Ƙungiyar Manoma, Masu Sarrafawa da Masu Kasuwancin Tumatir ta Ƙasa (NATPAN) reshen Jihar Kano, ya bayyana cewa ƙarancin kayan na yanzu na yanayi ne, saboda lokacin girbin kayan lambu ya riga ya wuce a yawancin wuraren da ake nomawa.
Ya ce wannan abu ne da ke faruwa a kowace shekara saboda rashin ingantattun hanyoyin adana kayan gwari, kuma ana sa ran farashin zai ragu idan aka fara girbin damina.
A halin yanzu, ɗauƙacin yankin Arewa na dogara ne wajen samun tumatir daga wasu yankuna a Jihar Kaduna, Jihar Katsina, Jihar Kuri’a Riba, da kuma wasu sassan Jihar Benue.
Lawan Adam, masanin tattalin arzikin noma mazaunin Kano, ya jaddada cewa mafita guda ɗaya tilo mai ɗorewa ita ce rungumar ingantattun hanyoyin adana kayan lambu.
Ya nuna cewa manoma na fama da asarar kayan gwari bayan girbi, wanda ke ba da gudummawa ga ƙarancin kayayyaki da tsadarsu a lokutan da ba na noma ba.
Ya yi gargaɗin cewa ci gaba da yin asara na iya sa manoma su bar sana’ar noman kayan lambu.
Hanyoyin adanawa da manoma ke amfani da su a halin yanzu, musamman bushewa da rana, sun riga sun zama tsofaffi kuma marasa tsafta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Attarugu Bukukuwan Sallah kasuwa kayan gwari Kayan miya tashin gwauron zabo tashin gwauron zabo ya bayyana cewa farashin kayan da aka sayar da farashin kayan lambu kayan gwari
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Yi Tanadi Na Musamman Ga Alhazanta A Mina
Alhazan Jihar Jigawa sun fara ayyukan hajji cike da kwarin gwiwa yayin da aka kaisu Mina daga birnin Makkah, inda za su wuce zuwa Dutsen Arafat domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.
Aikin hajji na farawa ne daga ranar 8 zuwa 13 ga watan Dhul Hajj a duk shekara, inda ake daukar alhazai zuwa sansanin Mina sannan su wuce zuwa Arafat, zuwa Muzdalifa, sannan Jamarat (Jamratul Akbah), kafin su dawo Makkah inda za su kammala da Dawafi.
Yawancin Alhazan da suka zanta da Rediyon Najeriya sun bayyana cewa, duk da wahalhalun da ke tattare da aikin hajji, sun kuduri aniyar gudanar da hajjin lafiya kuma cikin nasara.
Wasu daga cikin Alhazan daga kananan hukumomin Jahun da Kiyawa, Hajiya Maijidda Abdulhamid da Alhaji Mohammed Abdullahi Idris sun bayyana cewa tsoron Allah da kaunarsa ke basu kwarin gwiwar jure wahalhalun aikin hajji, kasancewar Allah Ya bada tabbacin karbar dukkan addu’o’i, don haka wajibi ne su jure domin babu wani alheri da ke zuwa cikin sauki.
Wani Alhaji daga Dutse, Murtala Sani Lama, ya bayyana cewa aikin hajji yana daga cikin ginshikan Musulunci, kuma kowanne musulmi mai hali yana da hakkin gudanar da shi. Ya kara da cewa a cikin Alkur’ani an bayyana cewa duk wata bukata da Alhaji ya roka za a amsa masa.
Ya kara da cewa wannan tabbacin kadai yana isar masa da kwanciyar hankali wajen shan wahalhalun aikin hajji komai yadda suka kasance.
Alhazan sun bayyana ra’ayin cewa kasancewar aikin hajji kira ne daga Allah kuma su baƙinsa ne na musamman, ba wani dogon tafiya ko zafi ko yawan mutane da zai hana su gudanar da ibada.
A cewar koyarwar Musulunci, duk wanda ya gudanar da aikin hajji yadda ya kamata, Allah yana gafarta masa dukkan zunubansa kuma yana bashi sabuwar dama kamar yadda aka haifi sabon jariri.
Haka kuma, a wata hira da Rediyon Najeriya, Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya ce dukkan abubuwan da suka wajaba domin jin dadin alhazan jihar an tanade su.
“An sanya ma tantin Alhazai na’urar sanyaya daki (air condition), tare da katifa da filo da kuma bargo ga kowane Alhaji. Kuma saboda zafin rana, mun saka firijin na ruwa tsakanin tantuna domin rage hatsarin kamuwa da matsanancin kishi.”
Labbo ya kara da cewa Alhazai za su rika samun abinci sau uku a rana tare da ruwan sha, da ‘ya’yan itatuwa da kuma lemun kwalba.
Ya shawarci Alhazai da su sanya tsoron Allah a zukatansu, yana mai cewa wannan ne mataki na farko na samun hajji mai kyau da tsari.
Usman Mohammed Zaria