Gwamnan Babban Bankin Iran ya wanda yake Ziyara a kasar China ya gabaatr da shawarar a kafa bankin hadin gwiwa a tsakanin kasashe mambobi a kungiyar Shangai.

Muhammad Riza Farzin ya isa kasar ta China ne domin halartar taron gwamnonin manyan bankunan kasashen da suke mambobi a cikin wanann kungiya, domin yin nazarin hanyoyin aiki tare a tsakaninsu da kuma musayar kudade.

Muhammad Riza Farzin ya kuma kara da cewa; Daga cikin ajandar taron kungiyar a China, akwai tattauna batun kafa bankin hadin gwiwa wanda daga cikin ayyukansa a akwai aiwatar da hada-hadar kudade da mu’amala a tsakanin Bankuna.”

Gwamnan babban bankin na Iran ya bayyana cewa, wannan kungiyar tana da matukar muhimmanci, domin tana kunshe da kasashe goma daga cikinsu akwai kasashe masu tattalin arziki a duniya, kamar China, India, da Rasha. Kuma mutanen da suke cikin kasashen kungiyar suna kai kaso 45% na jumillar mutanen duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Za A Yi Taron Kasa Da Kasa Akan Mahangar Imam Khumaini Dangane Da Falasdinu

 A gobe Litinin ne dai za a bude taron karawa juna sani anan Tehran mai taken; Imam Khumaini da batun Falasdinu” wanda zai sami halartar masana na cikin gida da kuma waje.

Jawabin bude taro zai fito ne daga shugaban kungiyar kare hakkokin al’ummar Falasdinu, Hujjatul-Islam Muhammad Hassan Rahimiyan, haka nan kuma magajin garin Tehran Ali Ridha Zakani zai gabatar da jawabi.

 Bugu da kari a yayin wannan taron za a girmama jagororin gwgawarmaya da su ka yi shahada da su ka hada, Sahid Sayyid Hassan Nasrallah, shahid Isma’ila Haniyya, sai shahid Yahya Sinwar. Shi ma shugaban kungiyar Ansarullah ta Yemen Sayyid Abdulmalik Husi yana cikin wadanda taron na Tehran za karrama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar
  • Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa
  • Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
  • Aragchi: Iran Tana Goyon Bayan Tattaunawa Saboda Hadin Kai Tsakanin Mutanen Lebanon
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran
  • Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
  • Kasashen AES zasu kafa kotun hukunta manyan laifuka ta kungiyar
  •  Iran  Ce Ta Farko A Duniya Wajen Dashen Koda
  •  Za A Yi Taron Kasa Da Kasa Akan Mahangar Imam Khumaini Dangane Da Falasdinu