Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester United ta sanar da ɗaukar ɗan wasan gaban ƙasar Brazil Matheus Cunha daga Wolverhampton Wanderes akan kuɗi fam miliyan 62.5, Cunha zai zama ɗan wasa na farko da Ruben Amorim zai saya a wannan bazarar yayin da yake ƙoƙarin sake gina ƙungiyar da ta ƙare a mataki na 15 a gasar Firimiya, Manchester United za ta kammala yarjejeniyar ɗaukar Cunha da zarar an buɗe kasuwar saye da sayarwar yan ƙwallo a ƙasar Ingila.

Ɗan wasan mai shekaru 26 ya rattaba hannu kan kwantiragin shekaru biyar a United tare da zaɓin ƙarin shekara, Cunha ya bar Wolves a matsayin ɗan wasa mafi tsada da ta taɓa sayarwa a tarihinta bayan da yarjejeniyar ɗaukar ɗan wasan ta kai ta fam miliyan 62.5, inda ta amince da tsarin biyan sama da shekaru biyu.

Duk da sha’awar da wasu ƙungiyoyin suka nuna akan Cunha, amma ya nuna sha’awar komawa Old Trafford da taka leda, yana mai imanin cewa United na ɗaya daga cikin manyan ƙungiyoyi a duniya kuma duk da rashin samun gurbi a gasar Zakarun Turai da tayi bayan rashin nasarar da suka yi a hannun Tottenham a wasan ƙarshe na gasar Europa.

Arsenal da Aston Villa na daga cikin waɗanda suka tattauna kan sayen ɗan wasan na Brazil a bana, ƙungiyoyin Saudi Pro League suma sun yi niyyar fitar da batun ɗaukar shi, ɗan wasan ya ƙulla yarjejeniya da Wolves daga Atletico Madrid a shekara ta 2022 kan kuɗi kusan fam miliyan 34 inda ya jefa ƙwallaye 15 sannan ya taimaka aka jefa shida a wasanni 33 da ya buga a gasar Firimiyar shekarar 2024/25.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

“Bisa ga hakan ne, Gwamnan jihar, Dakta Nasir Idris ya bayar da wannan tallafin don gudanar da shagalin sallar cikin walwala da Jin dadi”.

 

Shugaban ya gode wa Gwamnan jihar kan wannan kokarin da yayi na tunanin a zakulo mata uku a kowace rumfar zabe a duk mazabun kananan hukumomin 21 na jihar don basu tallafin N30,000 don gudanar da shagalin sallar Eid-kabir, “muna masa godiya a madadin matan da suka ci gajiyar tallafin”.

 

Daga karshe, Zuru ya yi kira ga sauran shugabanni da su yi koyi da Gwamnatin jihar Kebbi kan tallafa wa al’umma a jihar musamman a irin wannan lokaci ga wannan lokaci da jama’a ke da bukatar yin layya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
  • Nasarorin Shekaru Biyun Tinubu Shaida Ne Ta Shugaba Mai Hangen Nesa – Ministan Yada Labarai
  • Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
  • Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga
  • Magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga
  • Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
  •  Za A Yi Taron Kasa Da Kasa Akan Mahangar Imam Khumaini Dangane Da Falasdinu
  • Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • ‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa