Aminiya:
2025-07-24@03:50:54 GMT

Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne

Published: 2nd, June 2025 GMT

Wani yaro ɗan shekara 15 ya rasa ransa bayan mahaifinsa ya harbe shi bisa kuskure, yana zaton biri ne.

Wannan lamari mai ban tausayi ya faru ne a gonar magidancin inda shi da ɗan nasa suke aiki, a yankin Iye Ekiti da ke Ƙaramar Hukumar Ilejemeje ta Jihar Ekiti.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Ekiti,  Joseph Eribo, ya tabbatar da faruwar lamarin a yau a Ado-Ekiti.

Ya bayyana cewa manomin ya daɗe yana fama da hare-haren birai a gonarsa kuma ya kai bindiga domin kare amfanin gonarsa.

Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara An lakaɗa wa Mataimakin Firinsifal duka saboda hana satar a jarabawa

Binciken farko ya nuna cewa mahaifin ya lura da motsi a wata bishiya da ke kusa da shi, sai ya harba bindiga yana zaton biri ne. Bayan ya yi harbin sai ya gano cewa ya harbi dansa da ke kan bishiyar har lahira.

Tuni dai ’yan sanda suka tsare mahaifin domin yi masa tambayoyi yayin da bincike ke ci gaba kan wannan lamari mai ban tausayi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Harbe ɗansa

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi

Gwamna Bala Muhammad ya ƙaddamar da aikin gyare-gyare da sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi kan kuɗin da ya haura Naira biliyan bakwai, wanda ya haɗa da inganta kayan aiki, ofisoshi, da kuma gina sabon ofishin hukumar kula da harkokin majalisa.

A yayin ƙaddamarwar da aka gudanar ranar Talata, Gwamna Bala ya bayyana cewa wannan gyara na cikin shirin gwamnatinsa na sauya fasalin birane da samar da muhalli mai kyau ga ma’aikata domin sauƙaƙa aikinsu.

Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara

Ya ƙara da cewa tuni aka riga aka biya rabin kuɗin aikin domin tabbatar da cewa aikin ya kammala a kan lokaci.

Kwamishinan gidaje da muhalli, Danlami Ahmed Kawule, ya ce aikin zai ƙunshi gyaran zauren majalisar, ofisoshin mambobi, gina sabbin hanyoyin ruwa da wutar lantarki na masu amfani da hasken rana, da kuma gyara titunan cikin majalisar.

Tun da farko, mambobin majalisar sun koma ofishin tsohon mataimakin gwamna domin ci gaba da aikinsu yayin da ake gudanar da gyaran.

Gwamnan ya yaba wa fahimtar da ke tsakaninsa da majalisar, yana mai cewa hakan ne ke bai wa gwamnati damar aiwatar da ayyukan ci gaba.

Kakakin Majalisar, Abubakar Y. Suleiman, ya bayyana godiya bisa wannan ci gaba, yana mai cewa haɗin kai tsakanin majalisar zartarwa da majalisar dokoki na taka muhimmiyar rawa wajen kawo ci gaba a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu
  • Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da  Falasdinu a matsayin Mamba
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu
  • HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi
  • Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • MDD Ta Gargaɗi Isra’ila Kan Tilasta Wa Al’ummar Deir al-Balah Na Gaza Tashi