Sojojin Yemen sun kai jerin hare-hare har sau 4 kan filin jirgin saman Ben Gurion tare da wasu wurare masu muhimmanci a cikin Isra’ila

Sojojin Yemen sun sanar da aiwatar da hare-haren soji masu tsanani guda hudu a kan filin jirgin sama na Lod, wanda aka fi sani da “Ben Gurion” a haramtacciyar kasar Isra’ila, da kuma wasu muhimman wurare a yankunan Jaffa, Ashdod da Umm al-Rashrash a cikin Palasdinu da aka mamaye.

Rundunar sojin Yemen ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau cewa: Rundunarta ta kai wasu hare-haren soji masu inganci a kan tashar jirgin saman Lod da ke yankin Jaffa da aka mamaye da makamai masu linzami.

Dakarun sojin sun tabbatar da cewa: wannan farmakin ya samu nasarar cimma burin da aka sanya a gaba, wanda ya sa miliyoyin garken yahudawan sahayoniyya suka tsere zuwa maboyar karkashin kasa tare da janyo dakatar da ayyukan tashar jirgin saman.

Dakarun sojin Yemen sun yi nuni da cewa: Jiragen saman yaki mara matuki sun kai farmakin soji guda uku, inda suka auna wasu muhimman wurare uku na haramtacciyar kasar Isra’ila a yankunan Jaffa, Ashdod, da Umm al-Rashrash da ke yankin Falasdinu da aka mamaye, ta hanyar amfani da jiragen sama marasa matuka ciki guda uku.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar : Kasashen Faransa da Amurka ne ke kitsa mana hare-haren ta’addanci  

Shugaban Nijar Janar Abdourahmane Tiani ya ce har yanzu ana wa kasarsa zagon kasa ta fuskar tsaro musamman daga kasashen yamma.

Janar Tiani ya ambato kasar Faransa da tsohuwar gwamnatin Amurka a matsayin wadanda ke da hannu a matsalolin tsaro da ake fama da su.

Ya bayyana hakan ne a wata hira ta musamman da gidan talabijin na kasar RTN da aka watsa a yammacin ranar Asabar.

Ya dai yi bayyani ne kan batutuwa daban daban ciki har da halin da kasar ke ciki.

Shugaban kasar ta Nijar, ya kuma jinjinawa sojojin kasar dake bakin daga domin tsare kasar dare da rana, ya kuma isar da ta’aziyya ga sojojin da suka rasa rayukansu a kokarin kare kasar daga sha’anin ta’addanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Wani Kisan Kiyashi Kan Masu Bukatar Kayan Agaji
  • Shafin Watsa Labaran Amurka Ya Bankado Illar Da Sojojin Yemen Suka Yi Wa Jirgin Truman Na Amurka
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hari kan Falasdinawa Masu Karban Agajin Jin Kai A Rafah
  • Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara
  • Jirgin soji ya kashe mutane 20 a Zamfara
  • NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Yankunan Kasar Siriya Tare Da Kafa Wuraren Bincike
  • Nijar : Kasashen Faransa da Amurka ne ke kitsa mana hare-haren ta’addanci