Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara
Published: 2nd, June 2025 GMT
Aƙalla mutane 20 ne suka mutu bayan wani hari da jiragen sama na sojojin Najeriya (NAF) ya kai domin fatattakar ’yan bindiga a a Jihar Zamfara.
Jiragen sojin sun kashe wasu ’yan sa-kai bisa kuskure, a yayin da ’yan sa-kan suke ƙoƙarin fatattakar ’yan bindiga da suka kai hari a yankin Mani a Ƙaramar Hukumar Maru.
Jiragen sojin sun kai hare-haren ne domin fatattakar ’yan bindiga da suka kai wa manoma hari a kan babura da rana tsaka.
Mazauna yankin sun ce bayan ’yan bindiga sun sace manoma sama da 50 ne jirgin sojin ya amsa kiran gaggawa, amma aka samu kuskure ya kashe wasu ’yan sa-kai da ke ƙoƙarin fatattakar maharan.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-UwaWani mazaunin yankin ya shaida wa kafar BBC cewa, “Mun sanar da jami’an tsaro bayan harin, amma kawai sai muka ga jirgin ya zo ya kashe ’yan sa-kai na mu.”
Wani mazaunin garin ya ce, a yayin da jama’a ke ƙoƙarin taimaka wa wadanda aka kai wa hari, sai ga wani jirgin saman soji ya iso.
Ya ce, “’Yan bindigar sun tafi da mutane 50, amma yayin da muke ƙoƙarin kai ɗauki, sai muka ga jirgin soji, kuma ya fara harbin mu. Kowa ya gudu neman mafaka,” inda ya ƙara da cewa sun yi kamar matattu ne don su tsira.
Wani mazaunin kuma ya yi kira ga jami’an tsaro da su ƙara yawa, inda ya buƙaci a yankin amma su yi taka-tsantsan yayin gudanar da ayyukan.
Har yanzu sojojin Najeriya ba su ce komai ba game da lamarin.
Idan ba a manta ba, ire-iren wannan harin huskure ya faru a baya a yankin Jihar Zamfara. A watan Janairun 2025, wani harin jirgin saman sojin Najeriya ya kashe mutane 16 bisa kuskure, ciki har da ’yan sa-kai da manoma, a ƙauyen Tungar Kara a Jihar Zamfara, bayan an zaci su ’yan bindiga ne.
Hakazalika, a watan Disambar 2024, wani harin jirgin sama a Jihar Sakkwato ya kashe fararen hula 10 a sakamakon abin da Gwamnan jihar ya bayyana a matsayin harin kuskure kan fararen hula.
A watan Disamban shekarar 2023 wani jirgin soja ya kai irin harin inda ya kashe sama da fararen hula kimanin 100 a wurin taron Mauludi a yankin Tudun Biri da ke Ƙaramar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ke ƙoƙarin yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
Shugabannin Rundunar tsaro da Tinubu ya sallama sun hada da shugaban rundunar tsaro ta kasa Janar Christopher Musa da shugaban sojojin ruwa, Emmanuel Ikechukwu Ogalla da shugaban sojojin sama Hassan Abubakar.
Wadanda suka maye gurbin su da idanu ya koma kan hobbasar kwazon da za su nuna su ne shugaban rundunar tsaro Olufemi Oluyede, shugaban sojojin kasa Waidi Shaibu, shugaban sojojin ruwa Idi Abbas da shugaban sojojin sama S.K Aneke sai kuma shugaban rundunar leken asiri, EAP Undiendeye wanda ya ci-gaba da rike kujerar sa.
Yan Nijeriya sun jima suna kukan duk da kwarewa da gogewar jami’an sojojin Nijeriya da irin makuddan kudaden da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro a kowace shekara amma matsalar kullum gaba- gaba take kara yi.
Yankuna da dama a Nijeriya musamman a Arewa- Maso- Yamma, Arewa- Maso- Gabas da Arewa ta tsakiya sun zama lahira kusa a bisa ga yadda barayin daji ke garkuwa da mutane, kone garuruwa da yi wa jama’a kisan kare dangi.
Gagarumar matsalar wadda tuni ta zama tamkar ruwan dare a tsayin shekaru ta ci dimbin rayuka da dukiyoyin al’umma ba adadi ba tare da samun gagarumar nasarar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma ba.
Masana tsaro sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan sauye- sauyen. Wasu na ganin cewa sabbin jini za su iya kawo canji, yayin da wasu suka yi gargadin cewa sauya shugabanni kadai ba zai wadatar ba idan ba a yi gyaran tsari ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA