Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara
Published: 2nd, June 2025 GMT
Aƙalla mutane 20 ne suka mutu bayan wani hari da jiragen sama na sojojin Najeriya (NAF) ya kai domin fatattakar ’yan bindiga a a Jihar Zamfara.
Jiragen sojin sun kashe wasu ’yan sa-kai bisa kuskure, a yayin da ’yan sa-kan suke ƙoƙarin fatattakar ’yan bindiga da suka kai hari a yankin Mani a Ƙaramar Hukumar Maru.
Jiragen sojin sun kai hare-haren ne domin fatattakar ’yan bindiga da suka kai wa manoma hari a kan babura da rana tsaka.
Mazauna yankin sun ce bayan ’yan bindiga sun sace manoma sama da 50 ne jirgin sojin ya amsa kiran gaggawa, amma aka samu kuskure ya kashe wasu ’yan sa-kai da ke ƙoƙarin fatattakar maharan.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-UwaWani mazaunin yankin ya shaida wa kafar BBC cewa, “Mun sanar da jami’an tsaro bayan harin, amma kawai sai muka ga jirgin ya zo ya kashe ’yan sa-kai na mu.”
Wani mazaunin garin ya ce, a yayin da jama’a ke ƙoƙarin taimaka wa wadanda aka kai wa hari, sai ga wani jirgin saman soji ya iso.
Ya ce, “’Yan bindigar sun tafi da mutane 50, amma yayin da muke ƙoƙarin kai ɗauki, sai muka ga jirgin soji, kuma ya fara harbin mu. Kowa ya gudu neman mafaka,” inda ya ƙara da cewa sun yi kamar matattu ne don su tsira.
Wani mazaunin kuma ya yi kira ga jami’an tsaro da su ƙara yawa, inda ya buƙaci a yankin amma su yi taka-tsantsan yayin gudanar da ayyukan.
Har yanzu sojojin Najeriya ba su ce komai ba game da lamarin.
Idan ba a manta ba, ire-iren wannan harin huskure ya faru a baya a yankin Jihar Zamfara. A watan Janairun 2025, wani harin jirgin saman sojin Najeriya ya kashe mutane 16 bisa kuskure, ciki har da ’yan sa-kai da manoma, a ƙauyen Tungar Kara a Jihar Zamfara, bayan an zaci su ’yan bindiga ne.
Hakazalika, a watan Disambar 2024, wani harin jirgin sama a Jihar Sakkwato ya kashe fararen hula 10 a sakamakon abin da Gwamnan jihar ya bayyana a matsayin harin kuskure kan fararen hula.
A watan Disamban shekarar 2023 wani jirgin soja ya kai irin harin inda ya kashe sama da fararen hula kimanin 100 a wurin taron Mauludi a yankin Tudun Biri da ke Ƙaramar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ke ƙoƙarin yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700
Iftila’in ambaliyar ruwa a garin Mokwa a Ƙaramar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja ta yi ajalin mutane sama da 200, yayin da wasu sama da 500 suka bata.
Ambaliyar, wadda ita ce mafi muni a yankin cikin shekaru 60, ta shafi yankunan Tiffin Maza da Anguwan Hausawa, bayan ruwan sama kamar da bakin ƙwarya a ranar Laraba da ta gabata da daddare.
Ɗaruruwan gidaje sun lalace, inda mutane da yawa suka rasa matsugunansu.
Kafar yaɗa Labarai ta BBC ta ruwaito a ranar Litinin cewa yawan mutanen da suka mutu ya ƙaru zuwa sama da 200, kuma an dakatar da ayyukan ceto saboda hukumomi sun yanke ƙauna daga samun wasu da rai.
Babbar Sallah: Farashin kayan miya ya yi tashin gwauron zabo Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindigaMata da ƙananan yara na daga cikin waɗanda ambaliyar ta rutsa da su, ciki har da almajirai masu yawan gaske a makarantun tsangaya a yankin.
Musa Kimboku, wani jami’in yankin, ya tabbatar da dakatar da ayyukan ceto. Hakimin Mokwa, Muhammadu Aliyu, ya bayyana cewa ba a iya haƙo wasu gawarwaki ba saboda sun shiga “ta Kogin Neja.”
Basaraken ya ƙara da cewa za a fara tono gawarwakin da suka maƙale a karkashin ƙasa domin hana yaduwar cututtuka.
Wani magidanci da ya rasa matarsa da jaririnsu a ambaliyar, Malam Adamu Yusuf, ya ba da labari: “Ina kallo amma babu abin sa zan iya na taimako yayin da ruwa ya share iyalina. Na tsira saboda ina iya yin iyo.”
Saliu Sulaiman, wani mazaunin yankin, yace ya rasa kusan $1,500 – kudin da ya samu daga sayar da kayan gonarsa – kuma ya rasa matsuguninsa.
Mazauna yankin suna zargin cewa fashewar wani madatsar ruwa da ke kusa ta ba da gudummawa ga tsananin ambaliyar ruwa, wanda har yanzu hukumomi ba su tabbatar da hakan ba.
Karfin ruwan ambaliyar ya kasance mai tsanani har ma an ga gawarwaki a garin Rabba, wanda ke da nisan tafiyar awa daya daga Mokwa.
Musa Kimboku na Karamar Hukumar Mokwa ya umurci kauyukan da ke makwabta da su binne “duk wata gawa da suka samu.”
Kamfanin Dillancin Labarai na Faransa (AFP) ya ruwaito wani masunci na yankin Danjuma Shaba, wanda ya rasa gidansa na cewa, “Ba ni da wurin kwana. Gidana ya riga ya rushe.”
Farida Auwalu, wacce ita kadai ce ta tsira da cikin ’yan uwanta 16, ta rasa ’ya’yanta bakwai a ambaliyar. An gano gawarwakin huɗu daga cikin yara an binne su.
“Fatana shi ne in ga sauran gawarwaki kuma in yi musu jana’izar da ta dace don samun nutsuwa,” in ji ta.
Waɗanda suka tsira daga ambaliyar ruwa suna ƙoƙarin samun taimakon farko.
Hassan Umar, wani mazaunin yankin, ya shaida wa Al Jazeera cewa waɗanda abin ya shafa ba su da kuɗi ko abinci, inda akasarinsu ke kwana a fili.
Ambaliyar ta haddasa rugujewar gadar da ta haɗa yankunan Koshaba da Rabba, kimanin kilomita 7 daga garin Mokwa, inda ruwan ambaliyar ya hadu da Kogin Neja, inda aka gano gawarwaki da yawa a wurin da ruwan ya hadu da kogin.
Alhaji Tanko Bala, shugaban al’ummar Hausawa a Mokwa, ya bayyana a karshen mako cewa mafi yawan waɗanda abin ya shafa suna kwana a fili saboda babu ingantattun tanadi daga gwamnati don samar musu da matsuguni.
Ya soki sansanin da aka keɓe a makarantar firamare a matsayin wanda ba za a iya zama a ciki ba kuma ba shi da kayan bukatun yau da kullum, yana mai kira ga gwamnati da ta taimaka wa wadanda abin ya shafa da kayan kwanciya.