Sojojin Yemen sun kai jerin hare-hare har sau 4 kan filin jirgin saman Ben Gurion tare da wasu wurare masu muhimmanci a cikin Isra’ila

Sojojin Yemen sun sanar da aiwatar da hare-haren soji masu tsanani guda hudu a kan filin jirgin sama na Lod, wanda aka fi sani da “Ben Gurion” a haramtacciyar kasar Isra’ila, da kuma wasu muhimman wurare a yankunan Jaffa, Ashdod da Umm al-Rashrash a cikin Palasdinu da aka mamaye.

Rundunar sojin Yemen ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau cewa: Rundunarta ta kai wasu hare-haren soji masu inganci a kan tashar jirgin saman Lod da ke yankin Jaffa da aka mamaye da makamai masu linzami.

Dakarun sojin sun tabbatar da cewa: wannan farmakin ya samu nasarar cimma burin da aka sanya a gaba, wanda ya sa miliyoyin garken yahudawan sahayoniyya suka tsere zuwa maboyar karkashin kasa tare da janyo dakatar da ayyukan tashar jirgin saman.

Dakarun sojin Yemen sun yi nuni da cewa: Jiragen saman yaki mara matuki sun kai farmakin soji guda uku, inda suka auna wasu muhimman wurare uku na haramtacciyar kasar Isra’ila a yankunan Jaffa, Ashdod, da Umm al-Rashrash da ke yankin Falasdinu da aka mamaye, ta hanyar amfani da jiragen sama marasa matuka ciki guda uku.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ya bukaci Isra’ila ta saki wani ma’aikacin hukumar da ya ce sojojin Isra’ila sun kama a wani farmaki da suka kai a tsakiyar Gaza ranar Litinin.

Tedros Ghebreyesus ya ce sojojin sun jefa ma’aikatan agaji da iyalansu cikin hatsari a lokacin da suka shiga gidajensu da kuma babban dakin ajiyar kaya a Deir al-Balah.

Ya yi alƘawarin cewa WHO za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta a yankin.

Deir al-Balah dai na cike makil da Falasɗinawa da suka rasa matsugunansu a kusan shekaru biyu na yakin Gaza

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
  • Jirgin Rasha mai dauke da mutum 50 ya yi hatsari a China
  • Majalisar Dokokin Isra’ila Ta Kada Kuri’ar Sake Mamaye Yankunan Flasdinawa
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno
  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • Birgediya Janar Sabahi Fard Ya Jaddada Cewa: Duk Wani Sabon Hari Kan Iran Zai Fuskanci Martani Mai Gauni
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila