Sojojin mamayar Isra’ila sun sake yi kutse cikin garin Al-Qunaitra na kasar Siriya tare da kafa wurin bincike lamarin da ya fusata al’ummar yankin

Sojojin mamayar Isra’ila da suka sake yin Kutse cikin yankunan kasar Siriya sun gudanar da sintiri a yankunan tare da kafa shingen binciken ababan hawa tsakanin Khan Arnabeh da kauyen Jaba da ke lardin Quneitra.

Sintirin ya kunshi yahudawan sahayoniyya goma masu magana da harshen Larabci na ka’ida kuma suna sintirin ne a motoci kirar Hummer.

A cewar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Siriya, sojojin mamayar Isra’ila biyu kuma sun kutsa kai a tsakanin garuruwan Jaba da Khan Arnabeh, kusa da tsohon wurin binciken ababan hawa na Al-Saqri. Sun samu rakiyar motocin sojoji dauke masu rakiya kusan 20.

Sojojin suna gudanar da binciken motocin ne domin neman makaman da ke iya zama barazana ga tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila, lamarin da ya janyo cece-ku-ce tsakanin jama’a da bullar fargabar cewa: Wannan mummunan ci zarafi kan kasar Siriya zai iya ci gaba da janyo tada zaune tsaye.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman

Sojojin ruwan Iran sun sanar da cewa, wani jirgin ruwan Amurka na yaki da ya yi kokarin shiga tekun Oman, ya fuskanci gargadi daga sojojin ruwan Iran tare da tilasta masa janyewa.

Da saiyar yau Laraba ne dai jirgin sama mai saukar angulu mallakin sojojin ruwa, ya yi gargadi ga jirgin ruwan na Amurka da a karshe ya tilasta masa janyewa.

Da fari, jirgin ruwan yakin na Amurka ya yi wa jirgin sama mai saukar angulu na Iran barazanar kai masa hari, said ai duk da haka sojojin ruwan na Iran sun ci gaba da yin gargadi ga Amurkawan da su kar su shiga cikin ruwan tekun Oman.

Bayan wannan barazana ne aka aikewa jirgin ruwan Amurkan sako daga dakarun  tsaron sararyin samaniyar Iran  akan cewa, wannan jirin mai saukar angulu  yana da cikakkiyar kariya, don haka wajibi ne ga jirgin ruwan na Amurka mai suna “DDG Fitzgerald  ya janye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Yahudawan Sahayoniyya Sun Bullo Da Dabarar Kisa Kan Falasdinawa Musamman ‘Yan Gudun Hijira
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi