Bayan mintuna 90 na wasan ba tareda wani ya doke wani ba sai alkalin wasa ya bayar da damar bugun daga kai sai mai tsaron raga, Jamaica ta ci kwallaye 4 inda Nijeriya ta ci dukkan kwallaye 5 da yan wasan suka buga, hakan ya sa yaran na Eric Chelle suka lashe gasar Unity Cup ta bana da ta kunshi kasashen Ghana, Trinidad And Tobago, Jamaica da Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

Kyaftin din tawagar Super Eagles ta Nijeriya Ahmed Musa, ya auri matarsa ta 4, Asmau Moriki, a wani biki na sirri da aka gudanar a jihar Kano, Musa da amaryarshi Asmau sun zama mata da miji watanni kadan bayan haduwarsu, Musa ya bar sansanin tawagar Super Eagles dake birnin Landan domin ya halarci bikin wanda aka gudanar a birnin Kano.

Dan wasan dake taka leda a kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, ya shiga wasan da Nijeriya ta doke Ghana da ci 2-1 a minti 60 na wasan, Musa na daya daga cikin yan wasan da sukafi taka leda a tarihin tawagar kwallon kafa ta Nijeriya inda kuma ya zamo wanda yafi jefawa Nijeriya kwallaye a gasar kofin Duniya a tarihinta.

Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

Musa ya yi aurenshi na farko a shekarar 2013 inda ya auri Jamila, ma’auratan, wadanda suka haifi ‘ya’ya biyu sun rabu a shekarar 2017 bayan wata hatsaniya ta ma’aurata wadda ake alakantawa da burin da Musa kedashi na kara aure ya shiga tsakaninsu a wancan lokacin, jim kadan bayan rabuwar, ya auri Juliet Ejue, matar sa ta biyu, daga Ogoja a jihar Kuros Riba.

Har wayau aurensu da Juliet ya rabu duk da cewa ba a san takamaiman dalili ko lokacinda auren ya rabu ba, a shekarar 2021, ya auri Mariam wadda ita ce ta zama matarsa ta uku, sai yanzu kuma a ranar 30 ga watan Mayun 2025 aka daura auren Musa da Asmau Moriki wanda ya kasance aure na hudu da aka san tauraron dan wasan yayi, rahotanni sun bayyana cewa an gudanar da daurin auren cikin kwanciyar hankali a Kano kuma ya samu halartar ‘yan uwa da abokan arziki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An lakaɗa wa Mataimakin Firinsifal duka saboda hana satar a jarabawa
  • Gaza : Sabon kisan kiyashi a kusa da wurin rarraba kayan abinci
  • Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • ‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
  • An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
  • ‘Yan Wasan Kano Sun Rasu Sanadiyar Hadarin Mota Yayin Dawowa Daga Gasar Wasanni Ta Kasa
  • Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
  • Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica
  • Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa