Gwamnatin Tinubu na amfani da talauci a matsayin makami — Atiku
Published: 31st, May 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, da yin “amfani da talauci a matsayin makami” domin juya ’yan Najeriya.
Da yake jawabi a Abuja ranar Asabar a wajen lacca na cika shekaru 60 da haihuwar tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, mai taken “Amfani da Talauci a Najeriya,” Atiku ya yi zargin cewa gwamnati tana amfani da matsalar tattalin arziki don sarrafa ’yan kasa.
Ya ce, “Abin da muke fuskanta a halin yanzu a Najeriya shi ne gwamnati tana amfani da talauci a matsayin makami.”
Atiku ya yi nuni da bambancin yanayin rayuwa a yanzu da lokacin ƙuruciyarsa, inda ya ce a lokacin Kano tana cikin yalwar arziki, ba a saba ganin mutane marasa matsuguni ba.
Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba ‘’Yan bindigar birni sun karɓe shugabancin Najeriya — El-RufaiA cewarsa, yanzu lamarin ya canza, ta yadda talauci da rashin tsaro sun kai ga mutane suna barci a kan tituna da kuma karkashin gadoji a cikin birni Kano.
Har ma ya yi iƙirarin cewa an umarci wata hukumar jihar Kano da aka ɗora wa alhakin taimaka wa waɗannan mutane da ta dakatar da ayyukanta.
Atiku ya bayyana shigarsa cikin wata ‘gamayya siyasa’ don yaƙar wannan yanayi, yana mai cewa, “muna cikin wannan haɗin gwiwa don tabbatar da cewa ba za mu bari su ci gaba da amfani da talauci a matsayin makami ba.”
Da yake mai da martani ga kalaman Atiku, Rotimi Amaechi ya danganta ƙaruwar rashin tsaro a ƙasar da yawaitar talauci.
“Yunwa ba ta san ƙabila da addini ba, kuma gwamnatin yanzu ta sa mutane sun ƙara talaucewa, wanda hakan ya ƙara yawan rashin tsaro da aikata laifuka,” in ji Amaechi.
Tsohon ministan sufurin ya tunatar da ’yan Najeriya cewa ikon ƙarshe yana hannunsu, yana mai kira gare su da su yi amfani da damarsu ta kaɗa ƙuri’a don tumbuke shugabanni idan ba su gamsu ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Najeriya amfani da talauci a matsayin makami
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027
Hon. Nasiru ya kara da cewa Gwamna Radda ya yi kokari wajen yaki da matsalolin tsaro wanda suka addabi Jihar Katsina, inda ya bayyana cewa ana samun sauki sosai a wannan bangare.
Ya ce gwamnati ta gyara makarantu da asibitoci a fadin Jihar Katsina, inda aka maida su na zamani tare da daukar ma’aikatan lafiya da kuma malaman makaranta da yawansu ya kai 7,000, wanda ya ce ko haka aka tsaye suna da hujja da dalilin mara masa baya.
Idan za a iya tunawa a makon da ya gabata ne, ‘yan majalisun tarayya guda 15 dukkansu na jam’iyyar APC suka ayyana Gwamna Radda a matsayin wanda za su goya baya a zaben 2027.
Sai dai kuma ana dora ayar tambaya kan wadannan ‘yan majalisu da cewa sun yi riga Malam Masallaci, domin kafin su yanke irin wannan hukunci ya kamata su tuntubi wadanda suke wakilta domin gudun tutsu ranar zabe.
Yanzu dai abin jira a gani shi ne, Gwamna Radda zai maida biki, ma’ana dai shi ma ya amince kowane dan majalisa ya dawo kujerarsa ba tare da hammaya ba? Lokaci alkali!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp