Gwamnatin Tinubu na amfani da talauci a matsayin makami — Atiku
Published: 31st, May 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, da yin “amfani da talauci a matsayin makami” domin juya ’yan Najeriya.
Da yake jawabi a Abuja ranar Asabar a wajen lacca na cika shekaru 60 da haihuwar tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, mai taken “Amfani da Talauci a Najeriya,” Atiku ya yi zargin cewa gwamnati tana amfani da matsalar tattalin arziki don sarrafa ’yan kasa.
Ya ce, “Abin da muke fuskanta a halin yanzu a Najeriya shi ne gwamnati tana amfani da talauci a matsayin makami.”
Atiku ya yi nuni da bambancin yanayin rayuwa a yanzu da lokacin ƙuruciyarsa, inda ya ce a lokacin Kano tana cikin yalwar arziki, ba a saba ganin mutane marasa matsuguni ba.
Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba ‘’Yan bindigar birni sun karɓe shugabancin Najeriya — El-RufaiA cewarsa, yanzu lamarin ya canza, ta yadda talauci da rashin tsaro sun kai ga mutane suna barci a kan tituna da kuma karkashin gadoji a cikin birni Kano.
Har ma ya yi iƙirarin cewa an umarci wata hukumar jihar Kano da aka ɗora wa alhakin taimaka wa waɗannan mutane da ta dakatar da ayyukanta.
Atiku ya bayyana shigarsa cikin wata ‘gamayya siyasa’ don yaƙar wannan yanayi, yana mai cewa, “muna cikin wannan haɗin gwiwa don tabbatar da cewa ba za mu bari su ci gaba da amfani da talauci a matsayin makami ba.”
Da yake mai da martani ga kalaman Atiku, Rotimi Amaechi ya danganta ƙaruwar rashin tsaro a ƙasar da yawaitar talauci.
“Yunwa ba ta san ƙabila da addini ba, kuma gwamnatin yanzu ta sa mutane sun ƙara talaucewa, wanda hakan ya ƙara yawan rashin tsaro da aikata laifuka,” in ji Amaechi.
Tsohon ministan sufurin ya tunatar da ’yan Najeriya cewa ikon ƙarshe yana hannunsu, yana mai kira gare su da su yi amfani da damarsu ta kaɗa ƙuri’a don tumbuke shugabanni idan ba su gamsu ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Najeriya amfani da talauci a matsayin makami
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
Sojojin Yemen sun kai hari kan filin tashi da saukar jiragen sama na Lod da makami mai linzami nau’in ‘Palestine 2’
Dakarun sojin Yemen sun sanar da aiwatar da wani harin soji na musamman da aka kai kan tashar jirgin saman Lod da ke yankin Jaffa da aka mamaye da makami mai linzami kirar “Palestine 2”.
A cikin wata sanarwa da ta fitar da yammacin jiya, Rundunar Sojin Yemen ta bayyana cewa: Farmakin ya sanya miliyoyin garken yahudawan sahayoniyya tsere zuwa matsuguni karkashin kasa tare da dakatar da ayyukan tashar jirgin sama.
Sanarwar ta ce harin da aka kaiwa filin jirgin sama na Lod nasara ce ga al’ummar Falastinu da ake zalunta da kuma mujahidansu, da kuma mayar da martani ga kisan kiyashin da yahudawan sahayoniyya suka yi a zirin Gaza.
Sanarwar ta yi kira ga daukacin al’ummar Larabawa da na Musulunci da su fito kan tituna “don nuna goyon bayansu ga ‘yan uwansu a Gaza, saboda yadda suke fuskantar zalunci da wuce gona da iri na killacewa.