Aminiya:
2025-09-17@23:28:22 GMT

Gwamnatin Tinubu na amfani da talauci a matsayin makami — Atiku

Published: 31st, May 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, da yin “amfani da talauci a matsayin makami” domin juya ’yan Najeriya.

Da yake jawabi a Abuja ranar Asabar a wajen lacca na cika shekaru 60 da haihuwar tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, mai taken “Amfani da Talauci a Najeriya,” Atiku ya yi zargin cewa gwamnati tana amfani da matsalar tattalin arziki don sarrafa ’yan kasa.

Ya ce, “Abin da muke fuskanta a halin yanzu a Najeriya shi ne gwamnati tana amfani da talauci a matsayin makami.”

Atiku ya yi nuni da bambancin yanayin rayuwa a yanzu da lokacin ƙuruciyarsa, inda ya  ce a lokacin Kano tana cikin yalwar arziki, ba a saba ganin mutane marasa matsuguni ba.

Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba  ‘’Yan bindigar birni sun karɓe shugabancin Najeriya — El-Rufai

A cewarsa, yanzu lamarin ya canza, ta yadda talauci da rashin tsaro sun kai ga mutane suna barci a kan tituna da kuma karkashin gadoji a cikin birni Kano.

Har ma ya yi iƙirarin cewa an umarci wata hukumar jihar Kano da aka ɗora wa alhakin taimaka wa waɗannan mutane da ta dakatar da ayyukanta.

Atiku ya bayyana shigarsa cikin wata ‘gamayya siyasa’ don yaƙar wannan yanayi, yana mai cewa, “muna cikin wannan haɗin gwiwa don tabbatar da cewa ba za mu bari su ci gaba da amfani da talauci a matsayin makami ba.”

Da yake mai da martani ga kalaman Atiku, Rotimi Amaechi ya danganta ƙaruwar rashin tsaro a ƙasar da yawaitar talauci.

“Yunwa ba ta san ƙabila da addini ba, kuma gwamnatin yanzu ta sa mutane sun ƙara talaucewa, wanda hakan ya ƙara yawan rashin tsaro da aikata laifuka,” in ji Amaechi.

Tsohon ministan sufurin ya tunatar da ’yan Najeriya cewa ikon ƙarshe yana hannunsu, yana mai kira gare su da su yi amfani da damarsu ta kaɗa ƙuri’a don tumbuke shugabanni idan ba su gamsu ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Najeriya amfani da talauci a matsayin makami

এছাড়াও পড়ুন:

Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS

Hukumar ƙididdigar a Najeriya NBS ta bayyana cewa an samu raguwar hauhawar farashin kaya a watan Agusta idan aka kwatanta da watan Yulin da ya gabace shi.

Cikin sabbin alƙaluman da NBS ta fitar a ranar Litinin sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.76 a watan Agustan saɓanin watan Yulin, wanda ya nuna karo na hudu ke nan a jere hauhawar farashin yana sauka.

NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna

Rahoton na hukumar NBS na zuwa ne kwanaki bayan da Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin karya farashin kayan abinci ƙasar.

A watanin baya-bayan an riƙa samun raguwar hauhawar farashin kayyaki a ƙasar.

Ko alƙaluman da NBS ta fitar a watan Yuni, ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka zuwa kashi 22.22 daga 22.97 da aka samu a watan Mayu.

A baya dai dai an yi ta kiraye-kirayen gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakan rage hauhawarar farashi domin magance tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa