Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
Published: 23rd, March 2025 GMT
Kimanin shekaru 12 da suka wuce, wato a ranar 23 ga watan Maris din shekarar 2013, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da tunanin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, a karon farko, yayin da yake jawabi a wata jami’a dake birnin Moscow na kasar Rasha. Asalin tunanin ya shafi al’adun gargajiya na kasar Sin, wanda ya bukaci a samu jituwa, da daidaito tsakanin al’ummu daban daban, da tsakanin dan Adam da muhallin halittu.
Bisa tushen tunanin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya ne, kasar Sin ta gabatar da karin shawarwari, irinsu Ziri Daya da Hanya Daya, da wadanda suka shafi kokarin tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da cudanyar al’adu a duniya, ta yadda za a samu damar aiwatar da tunanin a harkokin dan Adam na fannoni daban daban.
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya taba nanata cewa, yayin da ake aiwatar da tunanin raya al’ummar dan Adam, ba za a ce wasu al’adu sun fi wasu ba, kuma ba za a nemi maye gurbin wani tsarin al’umma da wani na daban ba. Maimakon haka, abin da za a yi shi ne hakuri da bambancin kasashe daban daban, ta fuskokin tsarin al’umma, da al’adu, da matsayin ci gaban tattalin arziki, sa’an nan a raba riba, da hakki, da nauyin aiki a tsakanin su, don tabbatar da makoma mai haske ta al’ummar dan Adam. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: al ummar dan Adam
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
A nasa ɓangaren, mai bai wa Gwamnan Shawara Kan Al’ammuran Tsaro, Janar Dahiru Abdusalam (Mai Ritaya), ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana ɗaukar matakai tare da jami’an tsaro don samar da tsaro mai inganci.
Ya kuma bayyana cewa duk da matsalolin tsaro da ake fuskanta a hanyar Damaturu zuwa Gujba, jami’an tsaro na ƙoƙarin yin sintiri domin tabbatar da tsaro.
Janar Dahiru ya ce, “Koda yake muna fuskantar ƙalubale daga Boko Haram a yankunan wasu sansanin sojoji, jami’an tsaro na ci gaba da aikinsu domin kare yankin.”
Ya ƙara da cewa, “Muna taka-tsan-tsan musamman wajen daƙile karɓar haraji daga Boko Haram a wasu yankuna. Wannan al’amari yana da matuƙar wahala, amma muna fatan za mu samu nasara.”
Janar Dahiru ya tabbatar da cewa akwai tsaro a dukkanin sassan jihar tare da haɗin gwiwar sojoji, ‘yansanda, Civilian JTF da ‘yan sa-kai.
Ya kuma bayyana cewa za a fitar da sabbin dabaru cikin makonni masu zuwa domin yaƙar ‘yan ta’adda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp