Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
Published: 23rd, March 2025 GMT
Kimanin shekaru 12 da suka wuce, wato a ranar 23 ga watan Maris din shekarar 2013, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da tunanin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, a karon farko, yayin da yake jawabi a wata jami’a dake birnin Moscow na kasar Rasha. Asalin tunanin ya shafi al’adun gargajiya na kasar Sin, wanda ya bukaci a samu jituwa, da daidaito tsakanin al’ummu daban daban, da tsakanin dan Adam da muhallin halittu.
Bisa tushen tunanin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya ne, kasar Sin ta gabatar da karin shawarwari, irinsu Ziri Daya da Hanya Daya, da wadanda suka shafi kokarin tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da cudanyar al’adu a duniya, ta yadda za a samu damar aiwatar da tunanin a harkokin dan Adam na fannoni daban daban.
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya taba nanata cewa, yayin da ake aiwatar da tunanin raya al’ummar dan Adam, ba za a ce wasu al’adu sun fi wasu ba, kuma ba za a nemi maye gurbin wani tsarin al’umma da wani na daban ba. Maimakon haka, abin da za a yi shi ne hakuri da bambancin kasashe daban daban, ta fuskokin tsarin al’umma, da al’adu, da matsayin ci gaban tattalin arziki, sa’an nan a raba riba, da hakki, da nauyin aiki a tsakanin su, don tabbatar da makoma mai haske ta al’ummar dan Adam. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: al ummar dan Adam
এছাড়াও পড়ুন:
Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
Ministan harkokin wajen Omani Badr Albusaidi ya sanar da cewa, ba za a gudanar da zagaye na shida na tattaunawar nukiliya tsakanin Iran da Amurka ba.
Yau Lahadi ne aka shirya gudanar da zagaye na gaba na shawarwari a Muscat babban birnin kasar Oman.
A cikin wani sakon da ya wallafa a kan X (tsohon Twitter), Albusaidi ya tabbatar da sokewar, yayin da ya jaddada cewa “diflomasiyya da tattaunawa sun kasance hanya daya tilo ta samun zaman lafiya mai dorewa.”
“Tattaunawar Iran da Amurka, wadda aka shirya gudanar da ita a birnin Muscat ranar Lahadin nan, ba za ta gudana a yanzu ba.
Tattaunawar diflomasiyyar da aka faro kan shirin nukiliyar Iran, a watan Afrilu a shiga tsakanin masarautar Oman, ta wargaje biyo bayan mummunan harin da Isra’ila ta kai kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi, a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugabar harkokin wajen kungiyar EU Kaja Kalas a ranar Asabar, ya ce ci gaba da tattaunawa da Amurka a cikin danyen aikin da Isra’ila ke yi bai da wata fa’ida.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ce kalaman shugaban Amurka sun tabbatar da cewa matakin da Isra’ila ta dauka kan Iran ya samo asali ne daga goyon bayan da Washington ke baiwa gwamnatin Tel-Aviv kai tsaye.