Aminiya:
2025-09-18@08:23:36 GMT

Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja

Published: 24th, March 2025 GMT

Wata tanka ɗauke da man fetur ta kama da wuta yayin da ta ke sauke mai a gidan mai na A.A. Rano da ke Kontagora, a Jihar Neja.

Lamarin ya faru ne da da misalin ƙarfe 7 na daren ranar Lahadi kusa da Asibitin Gaba.

Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara

Shaidu sun ce gobarar ta fara ne yayin da ake sauke man fetur, lamarin da ya jefa jama’a cikin fargaba kasancewar sauran tankunan mai maƙare suke da fetur.

Jami’an kashe gobara sun garzaya wajen don shawo kan lamarin, amma har yanzu wutar na ci gaba da yaɗuwa.

“Babu wanda aka ruwaito ya rasa ransa, amma mutane sun tsere domin tsira da rayukansu,” in ji wani mutum, mai suna Abba Mohammed.

Ƙoƙarin jin ta bakin Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, ya ci tura zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: A A Rano Gobara Kontagora

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

A lokacin gudanar da bincike, an samu layin waya guda 21 da takardun rijistar layi guda 29 a wajen Suleiman, wanda ya ce yana harkar rijistar layin ne.

Ya amsa cewa shi ne ya bai wa waɗanda “aka sace” waya da lambar da aka yi amfani da ita wajen neman kuɗin fansa.

Binciken ya nuna cewa waɗannan mutanen suna cikin wani tsari na zamba wanda ake kira da Ponzi.

An kuma gano cewa ɗaya daga cikinsu ya haɗa baki da wanda aka ce an yi garkuwa da shi don su karɓi kuɗi daga sauran abokan harkarsu.

SP Abiodun ya ce bincike ana ci gaba da bincike domin kama sauran waɗanda ke da hannu a lamarin, yayin da aka riga aka gurfanar da waɗanda aka kama a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawa Na 2025
  • ’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja