Aminiya:
2025-05-01@00:16:26 GMT

Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba

Published: 24th, March 2025 GMT

Wata mata mai suna Krystena Murray ’yar Amurka, wadda ta ɗauki ciki tare da haife jariri namiji ba tare da sanin cewa ba ɗanta ba ne, ta fara ɗaukar matakin shari’a a kan wani asibitin da ke taimaka wa mata samun ciki ta hanyar dashen ɗantayi (IBF).

Matar tana zargin asibitin da yi mata dashen ɗantayin da ba nata ba, bayan an tilasta ta, ta mayar wa asalin iyayen jaririn ɗansu.

NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa

Krystena Murray, mazauniyar Jihar Georgia, ta ɗauki cikin ne bayan dashen ɗantayi na (IBF) da aka yi mata a asibitin masu neman haihuwa da ake kira Coastal Fertility Clinic, a watan Mayun 2023.

To amma daga baya an gano cewa, ɗantayin da ta rena a cikinta na wasu ma’auratan ne daban, kamar yadda majiyar BBC ta ruwaito. Hakan ya fito fili ne bayan da Murray ta haifi jaririn da bai yi kama da ita ko wanda ya ba ta gudumawar maniyyi ba.

Duk da haka, Madam Murray ta so a bar mata yaron, don ta ci gaba da renon sa har tsawon watanni, amma hukumomi suka bai wa ainahin iyayen dan ikon karɓen ɗansu.

A cikin wani bayani da ta sanar ta hannun lauyanta, Murray ta ce: “Na ɗauki jaririn nan a cikina, na kamu da son sa, na haife shi, sannan na shaƙu da shi sosai, irin shaƙuwa ta ɗa da uwa, amma yanzu an ƙwace shi. Ba zan taɓa fita daga wannan takaici ba.”

Murray wadda baturiya ce, ta haifi jaririn, wanda ya kasance baƙar fata a watan Disamban 2023.

Ta ƙi sanya hotunan jaririn a shafukan sada zumunta sannan ta ƙi bari ’yan uwa ko abokanta su gan shi.

Daga nan ne ta sayi abin gwajin gano halittar gado, wanda za ta iya yin gwaji a gida.

Sakamakon da ta samu a watan Janairun 2024 ya tabbatar mata cewa, jaririn ba shi da alaƙa da ita, kamar yadda ta bayyana a koken da ta rubuta a kan asibitin.

Bayan wata ɗaya, ta sanar da asibitin game da lamarin. Asibitin ya sanar da asalin iyayen jaririn, waɗanda su kuma suka kai ƙara domin karɓar ɗan nasu, lokacin da yake da wata uku a duniya.

Dole ta sa Murray ta miƙa jaririn bayan lauyoyinta sun tabbatar mata cewa, ba za ta samu nasara ba, idan ta je kotu da nufin a bar mata jinjirin.

A halin yanzu jaririn na hannun iyayensa na asali a wata jiha, inda suka sauya masa suna. Koken da Murray ta shigar ya bayyana cewa, har yanzu ba ta san ko asibitin Coastal Fertility ya bai wa wasu nata ɗantayin ne ko kuma a’a.

A wani saƙo da ya tura wa kafar talabijin ta CBS News, asibitin ya amince cewa, ya tafka kuskure, sannan ya nemi afuwa game da halin da ya jefa matar a ciki.

“Wannan ne kuskure ɗaya da muka yi, kuma bai shafi wasu mutanen da muka bai wa kulawa ba,” kamar yadda asibitin ya sanar a bayaninsa.

“A ranar da aka gano wannan kuskuren, mun sake yin nazari mai zurfi a kan ayyukanmu tare da ɗaukar matakan kariya domin kare masu zuwa neman magani a wurinmu ta yadda ba za a sake samun irin haka ba.”

A shekarun baya-bayan nan an shigar da ƙararrakin asibitocin maganin haihuwa da dama kan yin kuskure wajen dashen ɗantayin.

Dashen IBF wani tsari ne da ake haɗa ƙwan haihuwar mace da maniyyin namiji a kwalba kafin a dasa ɗantayin a cikin mahaifar mace domin reno a matsayin juna-biyu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA

Shugaban hukumar makamshin Nujkliya ta MDD ya zanda da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi kan al-amuran da suka shafi shirin nukliyar kasar Iran da kuma tattaunawar da ake gudana tsakanin ta da Amurka.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a tattaunawa ta wayar tarho tsakanin jami’an guda biyu a jiya Lahadi, Grossi shugaban IAEA ya bayyana cewa ya ji dadin yadda JMI ta zabi tattaunawa da AMurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya. Ya kuma bayyana cewa hukumarsa a shirye take ta gabatar da duk wani taimakon da JMI take bukata a yayin tattaunawar.

A nashi bangaren Abbas Araqchi ya bayyana cewa kasar Iran a shirye take ta bada hadin kai ga hukumar ta IAEA kamar yadda yarjeniyar NPT take bukata da kuma dokokin kasa da kasa.

Abbas ya fada masa inda aka kai ya zuwa yanzu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, a biranen Mascat na kasar Omman da kuma Roma na kasar Italiya.

Ya zuwa yanzu dai kasashen biyu sun gudanar da taro har sau uku dangane da shirin Nukliyar kasar ta Iran, kuma bangarorin biyu sun bayyana amincewarsu da yadda tattaunawar take tafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA