Aminiya:
2025-11-02@17:09:52 GMT

Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba

Published: 24th, March 2025 GMT

Wata mata mai suna Krystena Murray ’yar Amurka, wadda ta ɗauki ciki tare da haife jariri namiji ba tare da sanin cewa ba ɗanta ba ne, ta fara ɗaukar matakin shari’a a kan wani asibitin da ke taimaka wa mata samun ciki ta hanyar dashen ɗantayi (IBF).

Matar tana zargin asibitin da yi mata dashen ɗantayin da ba nata ba, bayan an tilasta ta, ta mayar wa asalin iyayen jaririn ɗansu.

NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa

Krystena Murray, mazauniyar Jihar Georgia, ta ɗauki cikin ne bayan dashen ɗantayi na (IBF) da aka yi mata a asibitin masu neman haihuwa da ake kira Coastal Fertility Clinic, a watan Mayun 2023.

To amma daga baya an gano cewa, ɗantayin da ta rena a cikinta na wasu ma’auratan ne daban, kamar yadda majiyar BBC ta ruwaito. Hakan ya fito fili ne bayan da Murray ta haifi jaririn da bai yi kama da ita ko wanda ya ba ta gudumawar maniyyi ba.

Duk da haka, Madam Murray ta so a bar mata yaron, don ta ci gaba da renon sa har tsawon watanni, amma hukumomi suka bai wa ainahin iyayen dan ikon karɓen ɗansu.

A cikin wani bayani da ta sanar ta hannun lauyanta, Murray ta ce: “Na ɗauki jaririn nan a cikina, na kamu da son sa, na haife shi, sannan na shaƙu da shi sosai, irin shaƙuwa ta ɗa da uwa, amma yanzu an ƙwace shi. Ba zan taɓa fita daga wannan takaici ba.”

Murray wadda baturiya ce, ta haifi jaririn, wanda ya kasance baƙar fata a watan Disamban 2023.

Ta ƙi sanya hotunan jaririn a shafukan sada zumunta sannan ta ƙi bari ’yan uwa ko abokanta su gan shi.

Daga nan ne ta sayi abin gwajin gano halittar gado, wanda za ta iya yin gwaji a gida.

Sakamakon da ta samu a watan Janairun 2024 ya tabbatar mata cewa, jaririn ba shi da alaƙa da ita, kamar yadda ta bayyana a koken da ta rubuta a kan asibitin.

Bayan wata ɗaya, ta sanar da asibitin game da lamarin. Asibitin ya sanar da asalin iyayen jaririn, waɗanda su kuma suka kai ƙara domin karɓar ɗan nasu, lokacin da yake da wata uku a duniya.

Dole ta sa Murray ta miƙa jaririn bayan lauyoyinta sun tabbatar mata cewa, ba za ta samu nasara ba, idan ta je kotu da nufin a bar mata jinjirin.

A halin yanzu jaririn na hannun iyayensa na asali a wata jiha, inda suka sauya masa suna. Koken da Murray ta shigar ya bayyana cewa, har yanzu ba ta san ko asibitin Coastal Fertility ya bai wa wasu nata ɗantayin ne ko kuma a’a.

A wani saƙo da ya tura wa kafar talabijin ta CBS News, asibitin ya amince cewa, ya tafka kuskure, sannan ya nemi afuwa game da halin da ya jefa matar a ciki.

“Wannan ne kuskure ɗaya da muka yi, kuma bai shafi wasu mutanen da muka bai wa kulawa ba,” kamar yadda asibitin ya sanar a bayaninsa.

“A ranar da aka gano wannan kuskuren, mun sake yin nazari mai zurfi a kan ayyukanmu tare da ɗaukar matakan kariya domin kare masu zuwa neman magani a wurinmu ta yadda ba za a sake samun irin haka ba.”

A shekarun baya-bayan nan an shigar da ƙararrakin asibitocin maganin haihuwa da dama kan yin kuskure wajen dashen ɗantayin.

Dashen IBF wani tsari ne da ake haɗa ƙwan haihuwar mace da maniyyin namiji a kwalba kafin a dasa ɗantayin a cikin mahaifar mace domin reno a matsayin juna-biyu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.

Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,

Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.

Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu

Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hada

fitattun da za ta fuskanci kakar bana.

Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.

Raunin ‘yanwasa da ke jinya

Raunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.

Bayan Liberpool na yoyo

A kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.

Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara

kakar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa