Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh
Published: 18th, May 2025 GMT
An zartar da hukuncin kisa a kan wasu mutane 3 da ake zargi da kai harin ta’addanci a hubbaren Shah Cheragh
Shugaban hukumar shari’a ta lardin Fars (a kudancin Iran) ya sanar da cewa: Kotun Musulunci a birnin Shiraz ta yanke hukunci kan wasu mutane 7 da ake tuhuma da hannu a harin ta’addancin da aka kai a hubbaren Shah Cheragh (Ahmad ibn Imam Musa al-Kazim, amincin Allah ya tabbata a gare shi).
Haka nan kuma yayin da yake ishara da hukuncin da aka yanke wa mutanen bakwai da suka kai harin ta’addanci a hubbaren Shahragh, Hujjat al-Islam Sayyid Sadrullah Raja’i Nasab ya ce: A cikin hare-haren ta’addancin da aka kai a hubbaren Shahragh, baya ga manyan wadanda suka kai harin da aka hukunta bisa ayyukansu; An kuma hukunta wasu mutane saboda goyon baya da kuma tarayya da suka wajen samar da makamai da alburusai. Sannan bisa taimakon matakan leken asirin da aka sanya a cikin ajandar mai bincike na musamman da jami’an tsaro bayan faruwan wadannan al’amura, an gano wadannan mutane, an kama su, kuma sannan an dakile shirinsu na ta’addanci.
Hukunce-hukuncen sun hada da hukuncin kisa ga wasu mutane uku da aka samu da laifin “taimakawa wajen yada barna a kan doron kasa,” kuma an bayyana wadanda ake tuhumar a matsayin “masu kitsa” ayyukan ta’addanci. An kuma yanke musu hukuncin daurin shekaru 25 a kan kowane wanda ake tuhuma bisa zargin “taimakawa wajen gudanar da barna.”
An yanke wa wani dan ISIS hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari, wani kuma shekaru 10 da kwana daya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: wasu mutane
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya
“Idan za ku yi adalci a gare mu, a cikin makonni biyu da suka gabata, za ku ga cewa sojojin suna samun nasara wajen karya lagon ‘yan ta’adda, inda suka kashe su tare da tarwatsa sassaninsu,” in ji ministan.
A karshen makon da ya gabata, wadanda ake zargi ‘yan ta’adda na Boko Haram sun dasa na’urorin fashewa a Unguwar Guzamala na Jihar Borno, inda suka kashe mutane tara.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp