Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh
Published: 18th, May 2025 GMT
An zartar da hukuncin kisa a kan wasu mutane 3 da ake zargi da kai harin ta’addanci a hubbaren Shah Cheragh
Shugaban hukumar shari’a ta lardin Fars (a kudancin Iran) ya sanar da cewa: Kotun Musulunci a birnin Shiraz ta yanke hukunci kan wasu mutane 7 da ake tuhuma da hannu a harin ta’addancin da aka kai a hubbaren Shah Cheragh (Ahmad ibn Imam Musa al-Kazim, amincin Allah ya tabbata a gare shi).
Haka nan kuma yayin da yake ishara da hukuncin da aka yanke wa mutanen bakwai da suka kai harin ta’addanci a hubbaren Shahragh, Hujjat al-Islam Sayyid Sadrullah Raja’i Nasab ya ce: A cikin hare-haren ta’addancin da aka kai a hubbaren Shahragh, baya ga manyan wadanda suka kai harin da aka hukunta bisa ayyukansu; An kuma hukunta wasu mutane saboda goyon baya da kuma tarayya da suka wajen samar da makamai da alburusai. Sannan bisa taimakon matakan leken asirin da aka sanya a cikin ajandar mai bincike na musamman da jami’an tsaro bayan faruwan wadannan al’amura, an gano wadannan mutane, an kama su, kuma sannan an dakile shirinsu na ta’addanci.
Hukunce-hukuncen sun hada da hukuncin kisa ga wasu mutane uku da aka samu da laifin “taimakawa wajen yada barna a kan doron kasa,” kuma an bayyana wadanda ake tuhumar a matsayin “masu kitsa” ayyukan ta’addanci. An kuma yanke musu hukuncin daurin shekaru 25 a kan kowane wanda ake tuhuma bisa zargin “taimakawa wajen gudanar da barna.”
An yanke wa wani dan ISIS hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari, wani kuma shekaru 10 da kwana daya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: wasu mutane
এছাড়াও পড়ুন:
Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara
Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.
Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.
Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.
Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.
Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.
Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp