Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

“Wannan ci gaban zai kuma taimaka wajen kara habaka tattalin ardikin da ke a yankin na Arewa maso Gabas, wanda hakan ya zame mana wajbi, mu sake dawo wajen yin aikin domin aikin ya ci gaba da tafiya,” A cewar Ojulari.

Kan batun rikicin da yaki ci, yaki cinyewa a tsakanin Kamfanin na NNPCL da kuma rukunomin Kamfanin Dangote Ojulari ya bayyana cewa, ana ci gaba da kokari domin a kawo karshen rikicin.

“Dangote ya bayar da gagarumar gudunmawa wanda kuma, ya cannaci a yaba masa, za mu kuma yi hadaka domin mu tabbatar da, mun ci gaba da samar da wadataccen Man Fetur ga ‘yan kasar nan,” Inji Sabon Shugaban.

“Ana samun masalaha kan komai ne, ta hanyar tattaunawa za mu yi aiki kafada da kafada, domin amfanin ‘yan Nijeriya,” A cewar Ojulari.

Kazalika, da yake yin tsokaci kan batun samun raguwar farashin Danyen Mai a kasuwar duniya wanda hakan ya sanya burin samun kudaden shiga na kasar ya ragu, ya sanar da cewa, hakan ya shafi kasafin kudin kasar, duba da cewa, akasarin hasashen kasar ya dogara ne, kan samun kudin shiga na Man.

Ya sanar da cewa, NNPCL na kan aikin rage kashe kudaden gudanar da ayyukansa, wanda hakan zai bai wa Kamfanin damar yin amfani da kudaden shigar da yake samu, ta hanyar sayar da Man Fetur da na Iskar Gas.

Kan korafin da wasu yan kasar ke yi, kan rashin raguwar farashin Man Fetur da ake sayarwa a kasar, duk da cewa, farashinsa ya ragu a kasuwar duniya ya ce, Dilolin Man na bukatar lokaci, domin rage farashinsa.

“Idan Dilalan sun sayi Man kafin farashinsa ya ragu, suna bukatar su sayar da shi ne, kan tsohon farashi, amma idan sun saye shi kasa da sabon farashi, muna sa ran farashin ya sauka wanda zai nuna cewa, an samu sauyi,” Inji Ojulari.

A cewar NNPCL, tarin aikin na neman Man na Kolmani, an faro shi ne, tare da Kamfanin Mai na Shell a 1970, amma daga baya, aka yi watsi da aikin domin ba samu wata gagarumar cimma nasara ba.

Sai dai, daga baya an sake dawo da aikin ta hanyar Kolmani Riber 2, 3, and 4 a shekarar 2019, wanda hakan ya sanya aka gano Gangunan Danyen Mai biliyan daya da kuma Iskar Gas biliyan 500.

NNPC a ya sanar da cewa, a 2019 ya sake gabata da bukatar a yi amfani da kimiyyar zamani domin a ci gaba da aikin na nemna Man Kolmani.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu
  • Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
  • Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi
  • Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci
  • Majiyoyin Iran Sun Musanta Da’awar Karya Kan Neman Ziyarar Amurka Zuwa Cibiyoyin Sojojinta
  • Iran Ta Ce: Amurka Ba Ta Fadan Hakikanin Abubuwan Da Aka Tattauna A Zamanta Iran 
  • Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
  • Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba
  • Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin
  • Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma