Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
Published: 17th, April 2025 GMT
Majalisar dokokin jihar Zamfara ta mayar da dan majalisar dokokin jihar Zamfara da aka dakatar, Shamsudeen Hassan Basko, mai wakiltar mazabar Talata Mafara ta Arewa, bayan da ya nemi gafarar majalisar.
Hakan ya fito ne a wata sanarwa da sakataren yada labaran majalisar Bello Madaro ya raba wa manema labarai a Gusau.
A zaman da aka yi, Kakakin Majalisar, Alhaji Bilyaminu Ismail Moriki, ya karanta abin da ke cikin wasikar neman afuwar Basko, inda daga nan ne ya nemi shawarar majalisar ta gamayya inda ‘yan majalisar suka amince da dage dakatarwar.
Shugaban majalisar ya jaddada bude kofar majalisar na karbar irin wasikun neman afuwa daga sauran ‘yan majalisar bakwai da aka dakatar, inda ya ce irin wadannan matakai za su ba su damar dawo da su tare da samar da hadin kai a cikin majalisar.
Mambobin sun kuma yi masa maraba da komawa zauren majalisar, sannan sun bukaci sauran mambobin da aka dakatar da su yi koyi da ayyukansa domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban mazabarsu da jihar baki daya.
A takaitacciyar jawabinsa, Shamsudeen Hassan Basko ya bayyana matukar godiya ga majalisar bisa damar da ta samu ta mayardashi.
Basko ya yi alkawarin ci gaba da bin ka’ida, da’a na Majalisar, ya kuma sha alwashin nisantar da kansa daga duk wata kungiya ko yin tasiri da ke yunkurin bata mutunci da ikon majalisar.
Idan dai za a iya tunawa, a ranar 26 ga watan Fabrairun 2024 ne majalisar, bayan wani kudiri da shugaban masu rinjaye, Bello Mazawaje ya gabatar, ta dakatar da mambobinta takwas bisa saba wa kundin tsarin mulkin majalisar (Oda 10, Doka ta 9).
Matakin ladabtarwar dai ya samo asali ne daga zarge-zargen da ake yi masa, wanda ya hada da shigar karfi da yaji a ofishin magatakarda da zama ba bisa ka’ida ba, da dakile ayyukan majalisa, da kuma gudanar da ayyukan da ake ganin bai dace da ‘yan majalisar ba.
REL/AMINU DALHATU.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara da aka dakatar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20
Hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano ta dakatar da haska shirin Labarina, Dadin Kowa da wasu ƙarin fina-finan Hausa guda 20 a kafafen Internet ko gidajen talabijin.
Hukumar ta ce ta ɗauki matakin ne a ƙoƙarinta na tabbatar da ana bin dokar tace fina-finai sau da ƙafa tare da ƙara dora masana’antar Kannywood a kan saiti.
A cewar wata sanarwar da jami’in yaɗa labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya fitar da daren Lahadi, fina-finan da dakatarwar ta shafa sun haɗa da Labarina, Dadin Kowa, Manyan Mata, Garwashi, Jamilun Jidda da kuma Gidan Sarauta.
Sanarwar ta ce umarnin ya fito ne daga bakin shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, bayan wani zamanta da kuma tattaunawar da ta gudanar.
An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja Jami’in Sibil Difens ya mayar da N800,000 da wata Hajiya ta zubar a Adamawa Jerin fina-finan da aka dakatarSanarwar ta bayyana jerin fina-finan da dakatarwar kamar haka:
Ɗakin Amarya Mashahuri Wasiyya Tawakkaltu Mijina Wani Zamani Mallaka Kuɗin Ruwa Boka Ko Malam Wa Ya San Gobe Rana Dubu Manyan Mata Fatake Gwarwashi Jamilun Jiddan Shahadar Nabila Daɗin Kowa Tabarma Kishiyata da kuma Rigar Aro.Hukumar ta ce ta ɗauki gagarumin matakin ne domin tsaftace yadda ake sakin fina-finai barkatai ba tare da cika ƙa’idar da doka ta tanadar musu ba na kawo kowanne fim gabanta a tantance shi kafin a sake shi.
Sanarwar ta kuma ce doka ce ta ba Hukumar damar tace duk wani fim tare da lura da ayyukan ’yan masana’antar Kannywood matukar suna da rajista da hukumar a ko ina suke.
“A saboda haka, ana shawartar masu ɗaukar nauyin waɗannan fina-finai da su tabbatar da sun bi wannan doka ta dakatarwa tare da tsayar da saka wannan fina-finai a gidajen talabijin ko kafar internet.
“Haka kuma ana sanar da su cewa su miko fina-finansu ga hukumar domin tantance su tare da ba su shaidar inganci ta tacewa nan da sati ɗaya mai zuwa wato daga Litinin, 19 ga watan Mayu, 2025 zuwa 25 ga Mayu, 2025 domin gujewa fushin doka,” in ji sanarwar.
Tun bayan canjin da kasuwar fina-finai dai ta samu da ya sa kuɗaɗen da ake samu a sayar da fina-finai suka yi ƙasa sosai, galibin ’yan masana’antar Kannywood suka koma shirya fina-finai masu dogon zango domin a ci gaba da damawa da su.
Akan ɗora fina-finan ne a dandalin YouTube da wasu gidajen talabijin a mako-mako.