Aminiya:
2025-10-29@18:21:10 GMT

Tinubu ya janye afuwar da ya yi wa Maryam Sanda da masu manyan laifuka

Published: 29th, October 2025 GMT

Shugaba Bola Tinubu, ya janye afuwar da ya yi wa Maryam Sanda da masu laifukan da suka haɗa da kisan kai, safarar miyagun ƙwayoyi da sauransu.

Maryam Sanda, wadda aka yanke wa hukuncin kisa saboda zargin kashe mijinta, ba ta cikin sabon jerin sunayen wadanda aka yafe wa laifi. Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya tabbatar a ranar Laraba cewa an cire sunayen mutane kimanin 50 daga tsohon jerin bayan ce-ce-ku-ce daga jama’a.

“Bayan duba martanin jama’a, Shugaba Tinubu ya umarci a cire sunayen wadanda aka samu da manyan laifuka kamar garkuwa da mutane, safarar miyagun kwayoyi, da fataucin mutane daga jerin wadanda aka bai wa afuwa,” in ji Onanuga.

Ya kara da cewa an dauki wannan mataki ne “don mutunta ra’ayoyin jama’a, karfafa gwiwar jami’an tsaro, da tabbatar da adalci ga wadanda abin ya shafa da al’umma baki daya.”

Tsohon jerin sunayen da aka fitar ya haifar da suka daga jam’iyyun adawa da kungiyoyin kare hakkin dan Adam, wadanda suka bayyana matakin a matsayin amfani da ikon shugaban kasa ta hanyar da bata dace ba, kuma barazana ga tsarin shari’a. Sun yi gargadin cewa sakin manyan laifuka zai iya karfafa aikata laifi da kuma rage amincewa da doka.

Fadar shugaban kasa ta ce sabon umarnin yana nufin tabbatar da gaskiya da amincewa a tsarin bayar da afuwa. Shugaba Tinubu ya kuma umarci a dora aikin bayar da afuwa a karkashin ma’aikatar shari’a, tare da shigar da hukumomin tsaro da na shari’a a cikin tsarin don kauce wa irin wannan ce-ce-ku-ce a gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Afuwa Maryam Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

Shugaban ƙungiyar ta ƙasa, Frank Ogunojemite, ne ya sanya rattaba hannunsa a wasiƙar kamar yadda Jaridar PUNCH, ta samu kwafinta.

Shugaba ya bayyana cewa, ya kafa hujjar buƙatar soke tsarin, kan ƙalubalen da take fuskanta, na kashe kuɗaɗe masu yawa, musamman wajen safarar mayan Kwantainonin da ake shigoa da su daga ƙasashen da ke a Afirka ta Yamma

Ya ce, wannan tsarin ya sanya a yanzu, ana yiwa  masu safarar kaya zuwa cikin Tashar wani sabon cajin kuɗi da kuma jinkirin da suke samu, wajen shigar da kayan zuwa cikin Tashar.

Ogunojemite ya buƙaci Hukumar da ta tabbatar da wanzar da tsarin a matsayin na bai ɗaya a ɗaukacin Tashishin Jiragen Ruwan ƙasar.

“Muna gabatar da wannan buƙatar ce, domin mun yi amanna da cewa, a ƙarƙashin shuganacin shugaban Hukumar zai ci gaba da yin adalci da kuma tabbatar da ana bin ƙa’ida da kuma yin dubi ga lamarin ci gaban ƙasar nan, kan abinda ya shafi tafiyar da harkokin Jiragen Ruwan ƙasar,” Inji  Ogunojemite.

“A shirye muke domin yin tattaunawa da Hukumar da kuma sauran hukomin da abin ya shafa domin a lalubo da mafita, kan wannan buƙatar ta mu.” A cewar shugaban.

Sai dai, a martanin da Onyemekara ya jaddada cewa, babu gudu ba bu ja da baya na dakatar da wannan tsarin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano October 26, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji October 26, 2025 Labarai Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai October 26, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
  • Duk da ce-ce-ku-ce sunan Maryam Sanda na cikin wadanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • AA Zaura Ya Yi Kira Ga ’Yan Nijeriya Su Marawa Sauye-sauyen Shugaba Tinubu Baya
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin
  • Al-Burhan: Sojojin Sudan Sun Janye Daga El-Fasher Saboda Kare rayukan Fararen Hula
  • Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu
  • Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
  • “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”