Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29
Published: 30th, October 2025 GMT
Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya rattaba hannu kan sabuwar dokar da ta ƙirƙiri ƙarin ƙananan hukumomi 29 a jihar.
Wata takarda da Aminiya ta samu ta nuna cewa Mukaddashin Mataimakin Magatakarda na Majalisar Dokokin Jihar Bauchi, Musa Yerima, ya tura wannan ƙuduri zuwa Kwamitin Gyaran Kundin Tsarin Mulki, yana neman amincewar Majalisar Tarayya domin tabbatar da dokar a cikin gyaran kundin tsarin mulki da ake yi.
A halin yanzu, Jihar Bauchi na da ƙananan hukumomi 20 da kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya amince da su.
Da ƙarin waɗannan 29 da ake nema, jihar da ke da kimanin mutane miliyan 10 za ta samu jimillar ƙananan hukumomi 49 ke nan.
A cikin wasikar da Mataimakin Magatakarda ya aike wa Sanata Barau Jibrin, Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Duba Kundin Tsarin Mulki, ya ce: “Ina farin cikin sanar da ku cewa Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta amince da dokar da za ta ba da damar ƙirƙirar ƙananan hukumomi 29 a Bauchi, 2025.”
“Waɗannan ƙananan hukumomi ba za su fara aiki ba sai Majalisar Tarayya ta amince da dokar da za ta tabbatar da sunayen su kamar yadda Sashe na 8(5) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 ya tanada.
“Na kwatanta wannan bugun da dokar da Majalisa ta amince da ita, kuma na tabbatar da cewa wannan kwafi daidai ne da dokar da aka amince da ita,” in j wasikar.
Sunayen sabbin ƙananan hukumomin da ake son kirkira sun haɗa da: Balma, Bauchi ta Gabas, Bauchi ta Yamma, Beshongo, Bula, Burra, Chinade, Dagauda/Jalam da Disina.
Sauran su ne: Dogon Jeji/Jurara, Dass ta Yamma, Gadau, Galambi, Ganjuwa ta Gabas, Girawa, Gololo, Gwana, Isawa, Jama’a, Kankara, Lame, Lere, Madara, Sade, Sakuwa, Saye, Udubo, Yankari da Zungur.
Hedikwatocinsu sun haɗa da: Nasaru, Cibiyar Mata, Miri, Beni, Bununu, Chinade, Dagauda, Disina, Dogon Jeji, Lukshi, Gadau, Kangere, Faggo, Gololo, Futuk, Isawa, Nabordo, Akuyam, Karkara, Lame, Lere, Madara, Sade, Sakuwa, Hardawa, Udubo, Yelwan Duguri da Liman Katagum.
Yerima ya ƙara da cewa: “Wannan dokar an tura ta zuwa Shugaban Kwamitin Haɗin Gwiwa na Duba Kundin Tsarin Mulki na Majalisar Tarayya domin ci gaba da matakan da suka dace.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kundin Tsarin Mulki Jihar Bauchi da dokar da
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita.
Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar Hamas ta fadi cewa fashewar bama-bama da rushewar gidaje da mutuwar mutane da dama a daidai lokacin da ake tsananin ruwan sama da sanyi a yankin gaza ya kara tabbatar da kisan kiyashi isra’ila kan alummar Gaza, kuma ya kara tabbatar da gazawar tsarin duniya na daukar mataki don dakatar da ita.
Hamas ta ce isra’ila ce ke da alhakin duk wani bala’i da ake ciki a gaza, kuma ta soki kasashen duniya na yi gum da baki game da abubuwan dake faruwa ,don haka tana kira da a dauki matakin gaggawa domin janye killacewar da Isra’ila ta yi wa yankin don bada dama a shigar da kayayyakin agaji da kuma fara sake gina yankin.
Hazem Qassem kakakin kungiyar Hamas ya jaddada cewa ci gaba da rushewar gidaje da isra’ila ta rusa a hare-haren baya bayan nan yana kara nuna irin bala’in da falasdinawa ke ciki a yankin na rashin isar kayan agaji, don haka yayi kira da a dauki matakin gaggawa don dakatar da hare-haren, a fara sake gina yankin da samar da matsugunne da suka dace ga alummar Gaza
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 13, 2025 Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu December 13, 2025 Ali Nuhu, ya yaba wa Iran kan haskaka Musulinci ta hanyar fina-finai December 13, 2025 MDD ta amince da kudurin da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agaji a Gaza December 13, 2025 Benin ta fitar da sammacin kama dan fafutuka Kemi Seba December 13, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan December 12, 2025 Birtaniya Ta yi Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya December 12, 2025 Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare December 12, 2025 Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan December 12, 2025 Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci