An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Published: 26th, October 2025 GMT
A yau Asabar 25 ga wannan wata, ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar sun gudanar da liyafar murnar kebe ranar tunawa da kawo karshen mulkin mallakar Japan a yankin Taiwan, a dakin taro na Diaoyutai dake birnin Beijing.
Direktan ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin da ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Song Tao ya yi jawabi a gun liyafar cewa, an kebe ranar tunawa da kawo karshen mulkin mallakar Japan a yankin Taiwan a yayin cika shekaru 80 da kawo karshen mulkin mallakar Japan a yankin, wanda babban sakataren kwamitin tsakiya na JKS Xi Jinping ya gabatar, kuma zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar ya yi bincike tare da zartas da batun bisa dokoki, kuma wannan ya biya bukatun jama’ar kasar Sin da cimma burin dukkan kasar baki daya.
Kebe wannan rana, muhimmin aiki ne ga kasar Sin wajen tunawa da tarihin kasar da jaruman da suka ba da gudummawa ga kasar, da kuma sa kaimi ga tabbatar da ka’idar Sin daya tak a duniya, da kin amincewa da ‘yan aware na yankin Taiwan da masu tsoma baki kan harkokin cikin gida na kasar Sin, da kuma nuna goyon baya ga bangarori masu kaunar kasa da neman dinkuwar duk kasar Sin. Muna da karfi wajen yaki da ‘yan aware na yankin Taiwan, da sa kaimi ga samun zaman lafiya da bunkasuwa a tsakanin gabobi biyu na mashigin tekun Taiwan.
Ya kara da cewa, muna son zurfafa mu’amala da hadin gwiwa a tsakanin gabobin biyu, da raya al’ummar kasar Sin baki daya. Hakazalika, mun yi imani da sa kaimi ga samun dinkuwar duk kasar Sin, da kawo moriya ga jama’ar yankin Taiwan. Muna da karfi wajen tinkarar kalubale, da yin kokarin cimma burin farfadowar al’ummar kasar. (Zainab Zhang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: da kawo karshen mulkin mallakar Japan a yankin Taiwan ofishin kula da harkokin yankin Taiwan na a yankin Taiwan da
এছাড়াও পড়ুন:
Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki
Gwamantin Nigeria ta aike da jiragen yaki zuwa kasar Benin domin taimaka wa gwamnatin farar hula domin dakile yunkurin juyin mulkin da aka yi a kasar.
Aikin da jiragen yakin su ka fara yi, shi ne shimfida ikonsu a sararin samaniyar kasar Benin a ranar Lahadin da ta gabata,adaidai lokacin da sojoji da suke biyayya ga shugaba Patrice Talon su ka fafatawa da sojojin da suke kokarin mayar da doka da oda.
Ofishin shugaban kasar ta Nigeria, Ahmad Tininu ya kuma yi bayanin cewa; Daga cikin ayyukan da sojojin na Najeriya su ka yi a tare da hadin gwiwar takwarorinsu na Benin masu biyayya ga gwamnati, shi ne sanya idanu da kuma zama cikin ko ta-kwana domin aikewa da sojoji a kasa.
Ana kuma sa ran cewa sojojin kasashen Saliyo, Cote De Voire da Ghana za su isa Benin domin tabbatar da kare gwamnatin farar hula a karkashin kungiyar tattalin arziki ta yammacin Afirka ( Ecowas).
A mataki na karshe da sojojin Najeriya su ka tsoma baki a wata kasa ta yammacin Afirka shi ne 2017, yayin da shugaban kasar Gambia Yahya Jami’u, ya ki amincewa ya sauka daga karagar mulki duk da cewa bai ci zabe ba.
A duk lokacin da aka yi juyin mulki a cikin kasashen nahiyar Afirka,musamman a yammacinta, kasar Nigeria tana zama ta gaba wajen yin tir da shi. Juyin mulkin da ya gabata na kasar Guinea Bissau, ya sa gwamnatin Bola Ahmad Tinibu ta yi tir da shi, tare da yin kira da a mayar da kasar kan turbar demokradiyya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda December 9, 2025 Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025 Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci