Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC
Published: 29th, October 2025 GMT
Lauyan ICPC, Osuobeni Akponimisingha, ya gabatar da ƙarar neman a kwace kuɗin, yana sanar da kotun cewa, ICPC ta bi umarnin wucin gadi na kwace dalolin da ta yi a baya. Ya ce, an buga sanarwa ta jama’a inda aka gayyaci duk wani mutum wanda yake ganin akwai dalilin da zai hana ko kuma bai kamata a kwace kudin ba har abada, amma babu wanda ya amsa.
“Saboda haka, muna neman a ba da umarnin a kwace kudin har abada a mayar da su ga Gwamnatin Tarayya, saboda bin umarnin wucin gadi kuma babu wanda ya nuna adawa da hukuncin,” in ji Akponimisingha ga kotun.
Hukuncin ya biyo bayan umarnin wucin gadi da kotun ta bayar a ranar 30 ga Disamba, 2024, domin amsa bukatar da ICPC da Ma’aikatar tsaron farin kaya ta cikin gida (DSS) suka gabatar tare.
Takardar neman izinin, mai lamba FHC/ABJ/CS/1846/2024, kuma Usman Dauda, Daraktan Ayyukan Shari’a na DSS ya sanya wa hannu, ta nuna cewa an gano kudaden ne a lokacin bincike a gidan Dr. Ali da ke Kano.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Jami’an tsaro sun kashe ’yan bindiga 80 a Kebbi
Jami’an tsaron hadin gwiwar sun kashe fiye da ’yan bindiga 80 da suka yi yunƙurin kutsawa Jihar Kebbi ta iyakarta da Zamfara.
Rahotanni sun bayyana cewa, sojojin sama da na ƙasa sun gudanar da sumame a dajin Makuku, inda suka yi ruwan wuta kan sansanonin ’yan ta’adda, suka kuma kashe da dama daga cikinsu.
Dakarun sun kuma ceto mutane biyu da ’yan bindigar suka yi garkuwa da su.
A wata sanarwa da Daraktan Tsaro na Ofishin Majalisar Zartarwa ta Jihar Kebbi, Abdulrahman Zagga, ya fitar, an bayyana cewa dakarun sun yi nasarar daƙile wani mummunan hari da sama da ’yan bindiga 400 suka kai garin Ribah, inda aka yi musu mummunar ɓarna.
An kashe wasu makiyaya 10 a Kebbi Rikicin ADC: Sanata Nenadi ta zama shugaba a KadunaMai ba Gwamnan Jihar Kebbi shawara kan harkokin sadarwa da dabarun mulki, Abdullahi Idris Zuru, ya shaida wa manema labarai, cewa wannan aiki ya nuna tsayin daka da ƙarfin dakarun tsaro wajen yaƙi da ’yan ta’adda.
Ya ce, “Dakarun sun yi aiki tuƙuru don hana ’yan bindigar kutsawa cikin Kebbi. Wannan sumame wani ɓangare ne na ci gaba da ƙoƙarin daƙile ta’addanci da fashi da makami a fadin jihar.
“Sojojin Najeriya suna ci gaba da kai hare-hare a dazuka da yankunan da ke kan iyaka, musamman a dajin Makuku.”
Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar tana aiki kafaɗa-da-kafaɗa da hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayukan jama’a da dukiyoyinsu.