An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga
Published: 27th, October 2025 GMT
Kobi ta ce, an samu buƙata daga wajen mutane bakwai, inda aka tantance su domin fafata neman sa’a, daga baya mutane uku suka janye suka bar mutane huɗu domin fafata neman nasara a zaɓen.
“Bayan gudanar da zaɓen, Birgediya Janar Marcus Kokko Yake (Rtd) shi ne ya yi nasara.
“Za a gabatar da sakamakon nasarar da ya samu wa gwamnan domin amincewar da gabatar wa Gung-Zaar na farko takardar naɗinsa a matsayin Sarkin masarautar Zaar,” sanarwar ta shaida.
Wannan matakin dai na zuwa ne yayin da al’ummar Sayawa ke zanga-zangar adawa da yunƙurin gwamnatin jihar Bauchi ta Bala Muhammad wajen naɗa musu wani a matsayin Sarkin masarautar Sayawa wato (Gung Zaar).
Masu zanga-zangar dai sun bayyana cewa, Air Commodore Ishaku Komo (mai murabus) shi ne wanda suke so tuntuni wanda ya zama jagoransu bisa bin tsarin al’adarsu tun da jimawa. Masu zanga-zangar sun jawo hankalin gwamnatin jihar kan cewa, ta musu abun da suke so ba ƙaƙaba musu wani da ba sa so ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
Shugaban ƙungiyar ta ƙasa, Frank Ogunojemite, ne ya sanya rattaba hannunsa a wasiƙar kamar yadda Jaridar PUNCH, ta samu kwafinta.
Shugaba ya bayyana cewa, ya kafa hujjar buƙatar soke tsarin, kan ƙalubalen da take fuskanta, na kashe kuɗaɗe masu yawa, musamman wajen safarar mayan Kwantainonin da ake shigoa da su daga ƙasashen da ke a Afirka ta Yamma
Ya ce, wannan tsarin ya sanya a yanzu, ana yiwa masu safarar kaya zuwa cikin Tashar wani sabon cajin kuɗi da kuma jinkirin da suke samu, wajen shigar da kayan zuwa cikin Tashar.
Ogunojemite ya buƙaci Hukumar da ta tabbatar da wanzar da tsarin a matsayin na bai ɗaya a ɗaukacin Tashishin Jiragen Ruwan ƙasar.
“Muna gabatar da wannan buƙatar ce, domin mun yi amanna da cewa, a ƙarƙashin shuganacin shugaban Hukumar zai ci gaba da yin adalci da kuma tabbatar da ana bin ƙa’ida da kuma yin dubi ga lamarin ci gaban ƙasar nan, kan abinda ya shafi tafiyar da harkokin Jiragen Ruwan ƙasar,” Inji Ogunojemite.
“A shirye muke domin yin tattaunawa da Hukumar da kuma sauran hukomin da abin ya shafa domin a lalubo da mafita, kan wannan buƙatar ta mu.” A cewar shugaban.
Sai dai, a martanin da Onyemekara ya jaddada cewa, babu gudu ba bu ja da baya na dakatar da wannan tsarin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA