Aminiya:
2025-12-10@23:25:05 GMT

Tanka ta kife yayin da man fetur ya zube a kan titi a Neja

Published: 26th, October 2025 GMT

Wata tanka ɗauke da man fetur ta kife a kan hanyar Lambata zuwa Lapai zuwa Agaie da ke Jihar Neja, lamarin da ya haifar da tsoro da fargaba a tsakanin mazauna yankin.

An gano cewa tankar, wadda ta taso daga Legas tana kan hanyarta na zuwa Kano, ta kife ne da sassafe a garin Takalafiya da ke Ƙaramar Hukumar Lapai ta Jihar Neja.

Majalisa ta amince a ƙirƙiro sabbin jihohi 6 a Najeriya Matsalar kashe-kashe a Nijeriya ba ta da alaƙa da addini — Femi Kayode

Wani mazaunin garin Lapai, Mallam Mahmud Abubakar, ya shaida wa Aminiya cews lamarin ya faru kimanin kilomita biyu daga garin Lapai.

Ya ce kwanan nan aka gyara hanyar NNPCL, amma hanyar ta fara lalacewa cikin ƙanƙanin lokaci.

Wani ganau mai suna Mohammed Hassan Sonmaji ya ce, saurin zuwan jami’an kashe gobara na Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBUL) tare da na Hukumar Tsaro ta NSCDC ne ya taimaka wajen kauce wa mummunan hatsari a hanyar.

Ya ƙara da cewa jami’an ƙungiyar NUPENG reshen Lapai, sun isa waje don taimakawa wajen shawo kan lamarin.

An zagaye wani ɓangare da man ya zube domin gujewa aukuwar hatsari.

Da aka tuntubi Daraktan Sashen Bayani da Harkoki na Musamman na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Dokta Ibrahim Audu Hussaini, ya tabbatar da cewa babu abin zai auku.

Ya bayyana cewa tankar ba ta kama da wuta ba, kuma motocin kashe gobara na jami’ar IBBUL suna tsaye a wajen don shirin ko-ta-kwana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faɗuwa Hatsari

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda

 

 

 

 

 

 

Daga Bello Wakili

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ganawar sirri da gwamnonin jihohi shidda daga sassan ƙasar a ci gaba da tattaunawar da ake yi domin ƙarfafa batun tsaro a ƙasa.

Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Gwamna Monday Okpebholo na jihar Edo, Umar Namadi na Jigawa, Nasir Idris na Kebbi, Ahmed Ododo na Kogi, Lucky Aiyedatiwa na Ondo, da Ahmed Aliyu na  jihar Sokoto.

Taron, wanda ya ɗauki kusan mintuna 40, ya mayar da hankali ne kan muhimman matsalolin tsaro da ke shafar jihohinsu, duk da cewa ba a bayyana cikakkun bayanai ba.

Wakilin Rediyon Najeriya da ke fadar shugaban kasa ya ruwaito cewa wannan zaman na daga cikin kokarin shugaban kasa na ƙara haɗin kai da jihohi wajen magance matsalolin tsaro.

Wannan cigaban ya biyo bayan nasarar da Gwamnatin Tarayya ta samu na kubutar da dalibai 100 da aka yi garkuwa da su a Jihar Neja, baya ga wanda aka yi a Jihar Kebbi.

Ci gaba da irin waɗannan tattaunawa na shugaban kasa na nuna jajircewar gwamnati wajen tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a
  • Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Za a Yi wa Yara 194,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda