Pezeshkian: Hadin kan Musulmi zai iya dakile zalincin kasashen waje
Published: 27th, October 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce hadin kai tsakanin kasashen Musulmi yana da matukar muhimmanci wajen kare muradunsu da tsaronsu, daga duk wani cin zarafi daga kasashen waje.
Mista Pezeshkian ya yi wannan furuci ne a wata ganawa da Ministan Harkokin Cikin Gida na Oman Sayyid Hamoud bin Faisal al-Busaidi a Tehran yau Litinin.
Da yake nuni da kyakkyawar alakar da ke tsakanin Iran da Oman, wacce ya ce ta kasance bisa girmama juna da kuma kyautatawa.
Shugaban ya ce kasashen biyu ko yaushe suna goyon bayan junansu ta hanyar ci gaban yankin.
Ya yaba da rawar da Oman ta taka a ci gaban yankin, musamman a fannin sulhu da kuma karbar bakuncin tattaunawa tsakanin Iran da Amurka.
Iran da Amurka sun gudanar da tattaunawa kai tsaye har sau biyar a manyan biranen Italiya da Oman kan shirin nukiliya na Iran a farkon wannan shekarar kafin gwamnatin Isra’ila ta wargaza kokarin diflomasiyya ta hanyar kaddamar da yaki kan Jamhuriyar Musulunci a watan Yuni.
Shugaban ya bayyana fatan cewa ziyarar ministan Oman za ta kara karfafa hadin gwiwar kasashen biyu a fannonin kimiyya, tattalin arziki, al’adu, da siyasa.
A nasa bangaren, Busaidi ya bayyana dangantakar Iran da Oman a matsayin mai tarihi da gaskiya.
Ministan Oman ya bayyana fatan cewa kyakkyawar dangantaka mai karfi dake tsakanin Tehran da Muscat.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka ta tsare wani dan jarida musulmi saboda sukar Isra’ila October 27, 2025 Kashi 84% na ‘yan Faransa ba su gamsu da Macron ba a matsayin Shugaba October 27, 2025 Iran ta bukaci MDD ta nisanci nuna bangaranci game da masu keta dokokin duniya October 27, 2025 Kamaru : Paul Biya, ya lashe zaben shugaban kasa a karo na takwas October 27, 2025 An Nada Birgediya Janar Qarshi A Matsayin Mataimakin Babban Kwamandan Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci October 27, 2025 Hamas Ta Ce: Kungiyar Ta Ba Da ‘Yanci Ga Masu Shiga Tsakani Zabar Membobin Kwamitin Gudanar Da Gaza October 27, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe ‘Yan kasar Lebanon Biyu Tare Da Jikkatan Wasu Biyu Na Daban October 27, 2025 Amnesty International Ta Bukaci Bayyana Makomar Masu Fafutukar Kare Hakkin Bil’Adama Da Suka Bace A Uganda October 27, 2025 Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Yi Da’awar Kwace Karin Wasu Garuruwa A Sudan October 27, 2025 Qalibaf: Sakon Iran, Rasha da China ga MDD manuniya ce ta hadin gwiwa mai karfi October 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Makamashi: Iran Tana Da Sanayya Ta Ilimi Na Samar Da Hadari Domin Yin Ruwan Sama
Ministan makamashi na Iran Abbas Ali Abadi ya bayyana cewa; A halin yanzu Iran tana da ilimin aikewa da sanadarori cikin sararin samaniya da za su samar da hadari domin yin ruwan sama
Ministan makamashin na Iran wanda ya gabatar da jawabi a gaban majalisar shawarar musulunci ta Iran a jiya Talata ya ce; Aiki da aka yi a tsakanin gwamanti da majalisar dokoki da kuma cibiyoyin kwararru, shi ne ya kai ga samar da hukumar da take sanya idanu akan sauyin yanayi wanda ke iya samar da hadari da kuma yin ruwan sama.
Ministan ya yi Ishara da cewa sun bi matakai hudu domin ganin an isa wannan matsayin; Na farko dai shi ne; Amfani da na’urorin Radar domin bin diddigin yadda yanayi yake tafiya; Na biyu; yin kere-keren da su ka hada injinin samar da makamashi mai karfi; Sai kuma wasu fitilu da za su iya harba sanadarori na sanyi da zafi a sararin samaniya, da kuma jirage marasa matuki na musamman.
Bugu da kari ministan makamashin na Iran ya ce an kafa cibiyoyi 12 a fadin kasa domin sanya idanu akan yadda yanayi yake tafiya,wanda yana cikin mafi ci gaba a cikin wannan yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar China Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Akan Wani Babban Jami’in Banki December 10, 2025 Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran December 10, 2025 Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa December 10, 2025 Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Faransa ta ce da hannunta aka dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci