Aminiya:
2025-10-27@17:09:32 GMT

An rufe makarantu saboda ƙarancin man fetur a Mali

Published: 27th, October 2025 GMT

Duk makarantu a fadin ƙasar Mali da ke Yammacin Afirka za su ci gaba da kasancewa a rufe daga ranar 27 ga Oktoba zuwa 9 ga Nuwamba, sakamakon tsananin ƙarancin man fetur da ya janyo tsaikon harkokin sufuri da na yau da kullum.

Ministan Ilimi na ƙasar, Amadou Sy Savane ya sanar a ranar Lahadi cewa dukkan cibiyoyin ilimi za su dakatar da ayyukansu na tsawon makonni biyu saboda ƙarancin man fetur da ake fama da shi.

Paul Biya mai shekara 92 ya lashe zaɓen Kamaru Sule Lamiɗo na neman takarar Shugaban PDP na Ƙasa

Amadou Sy Savane ya shaida wa gidan rediyon gwamnati na ORTM cewa an shirya sake buɗe makarantu a ranar 10 ga watan Nuwamba.

Tsawon makonni dai, Mali na fama da ƙarancin man fetur sakamakon toshe hanyoyin sufuri da kungiyoyin ‘yan bindiga ke yi, musamman hanyoyin da manyan motocin dakon mai ke bi zuwa babban birnin ƙasar, Bamako.

Wannan lamari kacokam shi ne ya haifar da dogayen layuka a gidajen mai, yayin da motocin haya da babura suka daina zirga-zirga, abin da ya sanya titunan Bamako da suka saba tumbatsa da ababen hawa suka yi tsit.

Haka kuma, jami’o’i da manyan makarantun gaba da sakandire a babban birnin sun dakatar da karatu saboda dalibai da malamai sun kasa isa makarantu ƙarancin man fetur.

A gefe guda kuma, Ofishin Jakadancin Amurka da ke Bamako ya sanar a ranar 24 ga Oktoba cewa ƙananan ma’aikatansa da iyalansu za su bar ƙasar saboda ƙarancin man fetur da yayin da kuma matsalolin tsaro ke ƙaruwa.

A Juma’ar da ta gabata ce kuma ofishin jakadancin ya bayyana cewa ba zai iya ci gaba da gudanar da ayyukansa na yau da kullum ko na gaggawa a wajen Bamako ba, tare da shawartar jama’a su ci gaba da bibiyar shawarwarin tafiye-tafiye da gwamnatin Amurka ke bayarwa game da Mali.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: da ƙarancin man fetur

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Amurka Ya Ce: Za Su Dauki Matakin Soji Kan Kasar Venezuela Nan Gaba Kadan

Shugaban kasar Amurka Trump ya ce: Za su dauki matakin soji kan kasar Venezuela nan ba da jimawa ba

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi nuni da cewa kasarsa za ta iya fara yaki da “masu safarar miyagun kwayoyi nan ba da jimawa ba,” yana mai cewa, “Za su dauki mataki ta hanyar kutsawa ta kasa a kasar Venezuela,” yana mai nuni da yiwuwar shiga tsakani na soja ko ayyukan leken asiri.

A martanin da ya mayar, Shugaba Trump daga baya ya musanta rahotannin cewa: Jiragen yakin Amurka sun yi shawagi a kusa da kan iyakar Venezuela, yana mai jaddada cewa: “Ba gaskiya ba ne cewa: Amurka ta aika da jiragen yakin sama kusa da Venezuela.”

Trump ya shaida wa manema labarai a Fadar White House cewa: “Rahotanni daga kafofin watsa labarai game da aika jiragen yakin sama na B-1 zuwa kan iyakar Venezuela ba su dace da gaskiya ba.”

Trump ya kara da cewa: Gwamnatinsa ba za ta nemi Majalisar Dokoki ta “yi shelar yaki da masu safarar miyagun kwayoyi ba; za su kashe su kawai.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Iraki Ta Yi Allah Wadai Da Mamaye Yankin Yammacin Kogin Jordan Na Falasdinu October 24, 2025 ‘Yan Sandan Kasar Ghana Sun Tseratar Da ‘Yan Najeriya 57 Da Aka Yi Fasakwaurinsu October 24, 2025  Trump Ya Dakatar Da Tattaunawar Kasuwanci Da Kasar Canada October 24, 2025 Gaza: Tasirin Rashin Abinci Mai Gina Jiki Da Magani  Zai Ci Gaba  Har Zuriya Mai Zuwa October 24, 2025 Iran Ta Lashe Kambun Duniya Na Kokawar Gargajiya October 24, 2025 Pezeshkian: Iran za ta gwammace takunkumi a kan mika wuya October 24, 2025 Trump: Amurka na shirin kai hare-hare a Venezuela October 24, 2025 Ivory Coast: Ayyukan ma’adinai na fuskantar tsaiko  yayin da Ouattara ke neman wa’adi na 4 October 24, 2025 Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shi October 24, 2025 Larabawan Yankin Tekun Fasha Sun Caccaki Sabon Shirin Isra’ila A Kan Yammacin Kogin Jordan October 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙaddamar da Kyautar Jaruman Indomie Karo na 17: Matasan Najeriya Sun Fafata, An Samu Zakaru
  • Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 
  • “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai
  • Tanka ta kife yayin da man fetur ya zube a kan titi a Neja
  • Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
  • An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
  • ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Za Su Dauki Matakin Soji Kan Kasar Venezuela Nan Gaba Kadan