Mai mata ɗaya abin tausayi ne — Mijin Regina Daniels
Published: 27th, October 2025 GMT
Ɗan Majalisar Dattawa na daga Jihar Delta, Sanata Ned Nwoko ya ce yana tausaya wa manza masu mata ɗaya, saboda a cewarsa, auren mace fiye da ɗaya yana sama wa maza daidiato da natsuwa.
Sanata Nwoko shi ne mijin shahararriyar jarumai Regina Daniels — kuma Kirista ne amma yake da mata huɗu, ya bayyana haka ne a yayin hirar da ka yi da shi a gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi.
“Ina tausaya wa mai mata ɗaya, ƙaddara a ce mutum ne ke tsaye da ƙafa ɗaya — ai akwai wahala. Amma kana da biyu ko uku ko huɗu za ka fi samun daidaito. Wannan shi ne ɗan misalin da zan ba ka,” in ji Sanata Nwoko mai wakiltar Delta ta Arewa.
Da gabatar da shirin ya tunatar da shi cewa a matsayinsa Kirista, Baibul ya haramta auren fiye da mace ɗaya, sai sanatan, ya kada baki ya ce, “Tsohon Alƙawari ya halasta auren fiye da mata ɗaya, ni mai bin addini ne, amma ba wannan muke tattaunawa ba a nan.”
Saukar Farashin abinci: Manoma da gwamnati na nuna wa juna yatsa NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya?Sanata Nwoko ya jaddada cewa ko kaɗan ba ya yin nadamar auren mata huɗu da yi.
“Ba ni da wani abin da-na-sani. Kuma zan ƙara. Ya kamata mutum ya auri wanda yake so ya aura” in ji shi.
Ya kuma yi watsi da zargin tashin hankali tsakaninsa da matarsa, fitacciyar jarumar fina-finan Nollywood, Regina Daniels, a matsayin ƙarairayi.
“Ni ba mutum mai tashin hankali ba ne. Ina mutunta Matana kuma ina ƙaunar su da ’ya’yana,” in ji shi.
Bayanin nasa na zuwa ne bayan rahotannin da suka maye kafofin sada zumunta game da hatsaniya tsakaninsa da Regina Daniels ta wallafa wani katafaren gidan da ta ce ya gina mata,mita da sauran iyalansa.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: mace ɗaya Mata ɗaya
এছাড়াও পড়ুন:
Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
Jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo.
Jam’iyyar ta tabbatar da rasuwar ce a cikin wata sanarwa da sakatarenta yada labaranta na kasa, Kwamared Ini Ememobong, ya fitar.
Rahotanni sun ce Ewhrudjakpo ya yanke jiki ya faɗi a ofishinsa da ke gidan gwamnati, Yenagoa, a ranar Alhamis, inda aka garzaya da shi zuwa Cibiyar Lafiya ta Ƙasa (FMC) da ke Yenagoa.
Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis.
An haifi Ewhrudjakpo ranar ranar biyar ga watan Satumban 1965, a ƙauyen Ofoni da ke Ƙaramar Hukumar Sagbama, Jihar Bayelsa. Ya rasu yana da shekaru 60.
Kodayake ba a san ainihin dalilin faɗuwarsa ba, majiyoyi sun ce ya faɗi ne ba zato ba tsammani yayin da yake gudanar da ayyukan ofis, lamarin da ya sa dogarai da ma’aikatansa suka yi gaggawar taimaka masa.
Wasu majiyoyi da ke kusa da marigayin sun nuna cewa mutuwarsa na iya zama sakamakon bugun zuciya.
Lamarin ya haifar da ɗan tashin hankali a gidan gwamnati da kuma fadin Yenagoa, inda mazauna garin suka nuna damuwa game da mutumin da suke kira da “Mataimakin Gwamna Mai Aikin Dare.”
Sun ce sau da yawa yana yin aiki har dare ba tare da hutu ba.
A lokacin da ake rubuta wannan rahoto da yammacin jiya, gwamnatin Jihar Bayelsa ba ta fitar da wata sanarwa ba a hukumance a kan lamarin.
Kazalika, da mai taimaka wa mataimakin gwamnan kan yaɗa labarai, Doubra Atazi, da kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Ebiuwou Koku-Obiyai, sun ƙi yin bayani lokacin da aka tuntube su.
Sai dai a cikin sanarwarta, PDP ta bayyana kaduwa da alhini kan rasuwar mataimakin gwamnan, tana bayyana shi a matsayin “amintaccen ɗan jam’iyya kuma mai gaskiya.”
Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar PDP ta kadu matuƙa da labarin rasuwar Mataimakin Gwamnan Jihar Bayelsa kuma ɗan jam’iyya mai aminci, Mai Girma Sanata Lawrence Oborawharievwo Ewhrudjakpo, wanda rahotanni suka ce ya faɗi ya rasu a yau.
“Wannan labari mai tayar da hankali ya jefa Kwamitin Zartarwa na Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki, SAN, da kuma dukkan mambobin jam’iyyarmu mai girma, musamman mambobinmu masu aminci a Jihar Bayelsa, cikin baƙin ciki mai yawa.
“Tun yana raye, Sanata Ewhrudjakpo ya kasance ɗan siyasa mai gaskiya da daidaito wanda ya yi siyasa bisa ƙa’ida. Mutum ne da ya yi tsayin daka, jagora ne wanda rayuwarsa ta ta’allaka da imani, gaskiya da ƙarfin hali. Ya tsaya tsayin daka kan waɗannan dabi’u har zuwa ƙarshe.
“Muna cikin baƙin ciki matuƙa da rasuwar wannan jarumin siyasa mai gaskiya, kuma muna roƙon Allah ya ba shi hutu na har abada. Muna mika ta’aziyyarmu ga gwamnati da al’ummar jihar Bayelsa kan wannan babban rashin da ba za a iya maye gurbinsa ba.”