Bugu da kari, an shata wasu manyan manufofi game da shirin shekaru biyar-biyar na 15 da suka hada da gagarumar zurfafawa wajen samun ci gaba mai inganci, da ingantacciyar habaka dogaro da kai da karfin ci gaban kimiyya da fasaha, da cimma sabbin nasarori a cikin kara zurfafa gyare-gyare a gida gaba daya, da samun ci gaban al’adu da dabi’a a cikin al’umma a zahirance, da kara inganta jin dadin rayuwa, da samun manyan sabbin ci gaba wajen zurfafa shirin samar da kyakkyawar kasar Sin, da kuma kara samun ci gaba wajen karfafa garkuwar tsaron kasa.

 

A cikin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 14 (2021-2025), an kiyasta cewa, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin zai zarce yuan tiriliyan 35, ko kuma kimanin dala tiriliyan 4.93 na Amurka. In muka dauki matsakaicin ma’aunin tattalin arziki na shekara-shekara na kashi 5.5 cikin 100 daga 2021 zuwa 2024, kasar Sin ta bayar da gudummawar kusan kashi 30 cikin 100 na fadada tattalin arzikin duniya a kowace shekara.

 

A nan muke cewa, kasar Sin ta jaddada samar da ci gaba da kwanciyar hankali a dangantakarta da kasashen da take makwabta, da kasashen Afirka da ma duniya baki daya.

 

A farkon wannan watan, shugabar kula da cibiyar asusun bayar da lamuni ta duniya, Kristalina Georgieva ta yi gargadin cewa, ya kamata a yi sulhu a daidaita rikice-rikicen siyasa a gabas ta tsakiya, Gaza da Isra’ila; A Turai, Rasha da Ukraine; Buga Haraji ba misali, wanda duk wannan ke barazana ga tattalin arzikin duniya. Amma duk da ire-iren kalubalen da wadannan cikas din suka haifar, kasar Sin mai tattalin arziki ta biyu mafi girma a duniya ta ci gaba da tafiya a hankali wajen cimma burin ci gaba mai dorewa na Majalisar Dinkin Duniya.

 

Zaman taron karo na hudu, ya tabbatar da cewa, “akwai sauye-sauye masu sarkakiya da barazana a cikin yanayin da duniyarmu ke ciki a yau, amma tattalin arzikin Sin yana nan da juriya kuma kasar tana kan turbar ci gaba inda akwai damarmaki na habaka tattalin arziki sosai, duk da cewa yanayin rashin tabbas na ci gaba da karuwa”.

 

Wannan batu ya tabbatar wa al’ummar Sinawa da duniya cewa, masu tsara manufofin Sin sun san kalubalen da ke faruwa a duniya kuma sun shirya tsaf don magance kalubalen.

 

Sakamakon zaman taron, a fili yake, Sin ta kuduri aniyar ci gaba da saka tabbaci da kwanciyar hankali a duniya. A cikin gida, tsare-tsaren suna nuna sadaukarwa ga inganta karfin kasa da walwalar jama’a. A bangaren sauran kasashe kuwa, suna nanata cewa, kasar a bude take ga masu nufin kulla alaka, tare da haɗa kai, daidaito, da kuma cin gajiyar juna, wanda zai amfani kowa, ba ‘yan tsirarru ba.

 

Ga kasashe da suka gundura da mulkin danniya suke neman abokan hulda, za su iya dogara da Sin. Ta hanyar kiyaye kwanciyar hankali da tabbatar da zaman aminci a cikin gida da dorewar ci gaba, Sin ta zama kasa mai muhimmanci dake daidaita al’amuran duniya baki daya, wanda hakan na daya daga cikin manyan gudummawar da take bayarwa a yau.

 

 

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka? October 27, 2025 Ra'ayi Riga Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata October 23, 2025 Ra'ayi Riga Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin? October 23, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tattalin arzikin

এছাড়াও পড়ুন:

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

A baya bayan nan, kundin da aka amince da shi yayin cikakken zama na hudu na kwamitin kolin JKS na 20, ya tanadi tsare-tsaren musamman na fadada bude kofofin kasar ga sassan waje, da dora muhimmancin gaske ga samar da sabon yanayin hadin gwiwar cimma moriyar juna.

A halin yanzu, a hannu guda ana ganin zurfafar sabon zagayen juyin-juya-halin fasahohi, da sauyi a ci gaban masana’antu, a gabar da duniya ke bukatar bude kofa da rarraba gajiya sama da duk wani lokaci a baya. A daya hannun kuma, tsarin daukar matakan kashin kai da kariyar cinikayya na dada kamari, kuma duniya na fuskantar yanayin rashin daidaiton ci gaba da gibi a fannin jagoranci.

A wannan yanayi mai sarkakiya da duniya ke ciki, Sin ta nacewa kara fadada bude kofofinta, tana kuma ci gaba da karkata akalar nasarorinta kan turbar zamanantarwa ta Sin zuwa tsarin samar da gajiya ga ci gaban duniya na bai daya.

Shaida ta hakika ta nuna cewa, ba zai yiwu a raba tsakanin ci gaban Sin da na duniya baki daya ba, kana ba za a iya raba ci gaban duniya da na kasar Sin ba. Don haka, jigon samar da karin gudummawar Sin ga ci gaban tattalin arzikin duniya na da nasaba da babban tsarin bude kofofi daga mabanbantan sassa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5% October 26, 2025 Daga Birnin Sin An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing October 26, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai October 26, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba
  • Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
  • Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai
  • Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya
  • An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing
  • Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai
  • Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya
  • Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur