Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Published: 28th, October 2025 GMT
Bugu da kari, an shata wasu manyan manufofi game da shirin shekaru biyar-biyar na 15 da suka hada da gagarumar zurfafawa wajen samun ci gaba mai inganci, da ingantacciyar habaka dogaro da kai da karfin ci gaban kimiyya da fasaha, da cimma sabbin nasarori a cikin kara zurfafa gyare-gyare a gida gaba daya, da samun ci gaban al’adu da dabi’a a cikin al’umma a zahirance, da kara inganta jin dadin rayuwa, da samun manyan sabbin ci gaba wajen zurfafa shirin samar da kyakkyawar kasar Sin, da kuma kara samun ci gaba wajen karfafa garkuwar tsaron kasa.
A cikin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 14 (2021-2025), an kiyasta cewa, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin zai zarce yuan tiriliyan 35, ko kuma kimanin dala tiriliyan 4.93 na Amurka. In muka dauki matsakaicin ma’aunin tattalin arziki na shekara-shekara na kashi 5.5 cikin 100 daga 2021 zuwa 2024, kasar Sin ta bayar da gudummawar kusan kashi 30 cikin 100 na fadada tattalin arzikin duniya a kowace shekara.
A nan muke cewa, kasar Sin ta jaddada samar da ci gaba da kwanciyar hankali a dangantakarta da kasashen da take makwabta, da kasashen Afirka da ma duniya baki daya.
A farkon wannan watan, shugabar kula da cibiyar asusun bayar da lamuni ta duniya, Kristalina Georgieva ta yi gargadin cewa, ya kamata a yi sulhu a daidaita rikice-rikicen siyasa a gabas ta tsakiya, Gaza da Isra’ila; A Turai, Rasha da Ukraine; Buga Haraji ba misali, wanda duk wannan ke barazana ga tattalin arzikin duniya. Amma duk da ire-iren kalubalen da wadannan cikas din suka haifar, kasar Sin mai tattalin arziki ta biyu mafi girma a duniya ta ci gaba da tafiya a hankali wajen cimma burin ci gaba mai dorewa na Majalisar Dinkin Duniya.
Zaman taron karo na hudu, ya tabbatar da cewa, “akwai sauye-sauye masu sarkakiya da barazana a cikin yanayin da duniyarmu ke ciki a yau, amma tattalin arzikin Sin yana nan da juriya kuma kasar tana kan turbar ci gaba inda akwai damarmaki na habaka tattalin arziki sosai, duk da cewa yanayin rashin tabbas na ci gaba da karuwa”.
Wannan batu ya tabbatar wa al’ummar Sinawa da duniya cewa, masu tsara manufofin Sin sun san kalubalen da ke faruwa a duniya kuma sun shirya tsaf don magance kalubalen.
Sakamakon zaman taron, a fili yake, Sin ta kuduri aniyar ci gaba da saka tabbaci da kwanciyar hankali a duniya. A cikin gida, tsare-tsaren suna nuna sadaukarwa ga inganta karfin kasa da walwalar jama’a. A bangaren sauran kasashe kuwa, suna nanata cewa, kasar a bude take ga masu nufin kulla alaka, tare da haɗa kai, daidaito, da kuma cin gajiyar juna, wanda zai amfani kowa, ba ‘yan tsirarru ba.
Ga kasashe da suka gundura da mulkin danniya suke neman abokan hulda, za su iya dogara da Sin. Ta hanyar kiyaye kwanciyar hankali da tabbatar da zaman aminci a cikin gida da dorewar ci gaba, Sin ta zama kasa mai muhimmanci dake daidaita al’amuran duniya baki daya, wanda hakan na daya daga cikin manyan gudummawar da take bayarwa a yau.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA
কীওয়ার্ড: tattalin arzikin
এছাড়াও পড়ুন:
Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Seyyed Ali Khamenei ya ce duk da kalubale masu yawa da ake fama dasu a fadin, kasar tana samun “ci gaba, kuma tana kokari,” ta hanyar juriya, da kuma tabbatar da adalci ga mutanenta.
“Mmatsaloli a fadin kasar suna da yawa, amma al’umma, kowace rana, da juriya, kuma bisa yardar Allah kasar tana ci gaba, tana kokari,” in ji shi.
Jagoran ya bayyana hakan ne yau Alhamis yayin da yake jawabi ga dubban jama’a a bikin tunawa da ranar haihuwar Sayyada Fatima Zahra (SA) a Tehran.
Ayatollah Khamenei ya tabo wani bangare game da yakin farfaganda bayan harin watan Yuni da Isra’ila da Amurka suka kai wa Iran, wanda ya tilasta wa makiya su tsagaita wuta.
“A yau, bayan yakin da muka gani, muna tsakiyar yakin farfaganda da kafofin watsa labarai na makiya,” in ji shi.
Ya soki wadanda ke ikirarin sake barkewar yaki, yana mai cewa “Wasu suna ta kara nuna yiwuwar sake gwabza yaki, wasu kuma suna kara ruruta hakan da gangan don sanya mutane cikin rashin tabbas da damuwa, amma da yardar Allah, ba za su yi nasara ba.”
Ayatollah Khamenei ya ce ‘’burin makiyi” shi ne share tasiri, manufofi, da ra’ayoyin juyin juya halin Musulunci.
“Tsawon shekaru, azalumai na duniya sun yi kokarin canza asalin addini, tarihi, da al’adu na kasar Iran, amma juyin juya halin Musulunci ya sa duk wannan kokarin bai yi amfani.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannun kan yarjeniyoyi da dama a tsakaninsu December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu December 11, 2025 Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci