Aminiya:
2025-10-29@18:22:53 GMT

Super Falcons ta samu gurbin buga Kofin Afrika

Published: 29th, October 2025 GMT

Babbar tawagar ƙwallon ƙafa ta matan Najeriya Super Falcons ta samu tikitin buga gasar cin kofin nahiyyar Afrika ta mata ta 2026 da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci.

Super Falcons ta samu nasarar ne bayan tashi kunnen doki 1 da 1 da takwararta ta jamhuriyyar Benin a filin wasa na MKO Abiola da ke birnin Abeokuta a yammacin jiya Talata.

Gwamnatin Gombe ta fara tantance ma’aikata don kawar da na bogi An ceto jaririya ’yar mako daya da haihuwa da aka sayar a Anambra

Kunnen doki ya bai wa Najeriya nasarar shiga cikin jerin ƙasashen da zasu buga kofin na Afrika, bayan Falcons ta doke Benin da ci 2 – 0 a makon jiya a birnin Cotonou.

Hakan na nufin a wasanni biyu da ƙungiyyoyi suka fafata Najeriya ta samu nasara da ci 3-1.

Wannan dai shi ne karo na 14 da Falcons zata buga kofin nahiyyar Afrika da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci daga 17 ga watan Maris zuwa 3 ga watan Afrilu na 2026.

Najeriya ta lashe gasar sau 10 cikin gasanni 14 da aka buga a tarihi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ƙwallon ƙafa ta matan Najeriya Super Falcons

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun bayan sauya hafsoshin tsaro da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ne dai mutane da dama keta tofa albarkacin bakinsu, yayin da wasu ke ganin hakan zai taimaka wajen yaki da rashin tsaro, wasu kuwa na ganin duk jama’ar ja ce.

 

Shin ko sauya hafsoshin tsaro zai kawo karshen fargaban da al’umma ke yi?

NAJERIYA A YAU: Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas? DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kamaru za ta gurfanar da Issa Tchiroma a kotu kan zargin tayar da zaune tsaye
  • DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyya
  • An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
  • Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
  • Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
  • Ƙaddamar da Kyautar Jaruman Indomie Karo na 17: Matasan Najeriya Sun Fafata, An Samu Zakaru
  • Paul Biya mai shekara 92 ya lashe zaɓen Kamaru
  • Ƙaddamar da Kyautar Jaruman Indomie Karo Na 17 Yayin Da Zakarun Matasa Suka fafata daga karshe an samu zakaru
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya?