NSCDC ta yi alhinin mutuwar Kwamishinan Tsaron Gombe
Published: 26th, October 2025 GMT
Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) reshen Jihar Gombe, ta bayyana alhini bisa rasuwar Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na jihar, Laftanar Kanar Abdullahi Bello (mai ritaya).
Haka kuma hukumar ta bayyana jimami kan da ɗan sandan da ke tsaron kwamishinan, Sajan Adamu Husaini, da direbansu, wadanda suka rasu a wani mummunan hadarin mota da ya afku ranar Juma’a.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na NSCDC a jihar, SC Buhari Sa’ad, ya fitar, Kwamandan hukumar, Jibrin Idris, ya ce rasuwar babban rashi ce ba ga iyalan mamatan kawai ba, har ma ga Gwamnatin Jihar Gombe da al’ummar jihar baki ɗaya.
Kwamandan ya mika ta’aziyyarsa ga Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, da iyalan mamatan da abokan aikinsu, yana mai jaddada irin jajircewar da suka nuna wajen tabbatar da zaman lafiya a jihar.
“Kwamishina Abdullahi Bello da Sajan Adamu Husaini da direbansu sun bayar da gudunmawa mai muhimmanci ga sha’anin tsaro a Gombe. Rasuwarsu babban rashi ne ga kowa da kowa,” in ji Kwamandan Idris.
Ya yi addu’ar Allah Ya jikansu, Ya ba su Aljannatul Firdausi, tare da ba iyalan da suka bari hakurin jure wannan babban rashi.
Laftanar Kanar Abdullahi Bello kafin rasuwarsa, shi ne Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar Gombe, wanda aka san shi da jajircewa da kishin kasa wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jihar Gombe Kwamishina Jihar Gombe
এছাড়াও পড়ুন:
Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya
“Ban taba tunanin zan zama taurariya a duniya ba.”
Daga Yobe Zuwa Fagen Duniya
An haife ta a Jihar Kano kuma ta tashi a Yobe, labarin Nafisa ba shi da wuya kamar yadda yake da ban sha’awa.
Mahaifinta ya rasu tun tana jaririya, kuma mijin mahaifiyarta mai suna Alhaji Yusuf Umar Kaigama ya rene ta, wanda ya dasa mata dabi’u na tarbiyya da azama.
Tana kuma ɗauke da tsatson sarautar zuriyar sarakuna biyu masu daraja ta masarautar Kano, wato Sarkin Kano Ibrahim Dabo da Sarki Abdullahi Maje Karofi.
Amma bayan jinin sarautar da take ɗauke dasu, yunwar ta na neman ilimi ya sa ta zama daban.
A yanki da matsalar staro ta yi katutu wanda kuma yake dakushe duk wani ƙoƙarin karatun yara amma sai gashi ta zama gwarzuwa wannan abin alfahari ne sosai.
Nasara Ga Nijeriya
A gasar ƙarshe na ‘TeenEagle Global Finals’ – gasa mai tsauri, mai matakai da yawa wanda ya ƙunshi mahalarta sama da 20,000 daga sassan duniya – umarnin Nafisa na Ingilishi ya ba alkalai da takwarorinsu mamaki.
Ba wai kawai ta fi ɗalibai daga Amurka, Ingila, da Kanada ba – ta kuma sake fasalin labari game da ilimi a arewacin Najeriya.
Nasarar ta na ɗauke da nauyi sosai: ba lambar yabo ba ce ga yarinya ɗaya kawai; Wannan nasara ce ga miliyoyin matasan Nijeriya, musamman ‘yan mata, waɗanda ke yin mafarki duk da rashin daidaito da suke fuskanta.
“Nasarar da ta samu yana tunatar da duniya cewa ƙarfin Nijeriya ba shi da iyaka idan aka horar ta yara cikin basira, ba a kuma yi watsi da su ba.”
Samar Da Gwagwarmaya
Bayan nasarar da ta samu, Nafisa ta ƙaddamar da kamfen mai taken “Ku Rinƙa Turanci a koyaushe: A daina wasu harsunan da ba Ingilishi ba a makarantu.”
Saƙonta a bayyane yake: ƙwarewar Ingilishi, in ji ta, ba batun watsi da al’ada ba ne rungumar dama ce.
Ta zama mai ba da shawara ga amincewar harshe, yawon buɗe ido makarantu da kuma yin jawabi a majalisa inda ta buƙaci ɗalibai su yi amfani da Ingilishi a matsayin kayan aiki na haɗin gwiwar samun fahimtar juna a duniya.
Wannan matsaya ya jawo mata masoya a tsakanin gidajen yaɗa labaru, azuzuwa masu ruwa da tsaki a sassan yankin arewa maso gabas na Nijeriya.
Matsayinta Yafi a Auna
Tawali’u da hankali da kuma natsuwa da Nafisa ta yi ya sanya ta zama alamar ƙwazo na ƙasa.
A cikin duniyar da shahararru ke sha’awarta, tashinta ya zama shaida cewa hankali, horo, da alheri har yanzu suna ba da umarnin girmamawa.
Nasarar da ta samu ya sa ba a san ta ba: shigar da ita bangon Arewa – wanda ya sa ta zama mafi karancin shekaru da aka taba karramawa.
A yanzu ta tsaya kafaɗa da kafaɗa da jaruman al’adu, masu ƙirƙire-ƙirƙire, da ma’aikatan gwamnati waɗanda rayuwarsu ta fassara matsayin yankin arewa.
Hawa Hanyar Zama Gwarzuwa
Abin da ya sa tafiyar Nafisa ta fi ban sha’awa shi ne cewa tana wakiltar sabuwar fuskar ilimi – wanda ya samu ta hanyar juriya.
Nasarar da ta samu ya riga ya zaburar da sababbin ɗalibai waɗanda a yanzu suke ganin amfanin ilimi a matsayin hanyar alfahari, ba matsi ba.
A ajujuwa a faɗin jihohin Yobe da Kano, sunan ta ya zama abin ambato.
Malamai suna nusar da ita a cikin darasi. Iyaye suna gaya wa ‘ya’yansu, “Idan Nafisa za ta iya yin hakan, ku ma za ku iya.”
Nasarar da ta samu ya haifar da ɗa mai ido, wanda ya sa malaman makarantun gwamnati dana masu zaman kansu suka ƙara saka hannun jari a shirye-shiryen karatunsu da kuma kafa ƙungiyoyin ɗalibai masu muhawara.
“Ba kawai ta ci gasa ba,” in ji ɗaya daga cikin masu ba ta shawara.
“Ta sake saita yadda al’amura za su kasance a nan gaba.
Ƙarfi Da Ikon Kalmomi
Ga Nafisa, harshe ya fi abin za a samu nahawu da ƙamus – abu ne da ke zama garkuwa ga mutum.
Ita ce gada tsakanin keɓewa kuma shi ne bambanci tsakanin shiru da magana.
Burinta, in ji ta, shi ne na yi nazarin ilimin harshe kuma wata rana ta zama mai ba da shawara kan ilimi a duniya – “taimaka wa matasan Afirka su sami muryarsu a cikin duniyar da muke ciki.”
Wannan mafarki, kamar labarinta, yana magana da wani abu mafi girma fiye da abin da ta bayyana.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Bankin Providus October 25, 2025 Labarai Hukumar NASENI October 25, 2025 Labarai Daɓid Adeyemi October 25, 2025