Aminiya:
2025-12-11@19:58:13 GMT

Dangote na shirin faɗaɗa matatarsa don zama mafi girma a duniya

Published: 26th, October 2025 GMT

Alhaji Aliko Dangote, na shirin faɗaɗa matatar mansa domin ta riƙa tace gangar mai miliyan 1.4 a kowace rana.

A halin yanzu, matatar tana tace gangar mai 650,000 a rana, amma Dangote, ya bayyana cewa suna shirin ƙara adadin cikin shekaru uku masu zuwa.

Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki El-Clasico: Real Madrid ta doke Barcelona da ci 2

Ya bayyana haka ne yayin wani taro da manema labarai a ranar Lahadi, inda ya ce faɗaɗa aikin zai sa matatar ta zama mafi girma a duniya.

“Wannan shiri yana nuna yadda muke da cikakken shiri a Afirka da kuma dogaro da makomar Najeriya a ƙarƙashin shugabancin Bola Tinubu,” in ji shi.

Ya bayyana cewa aikin zai gudana cikin sauƙi saboda kamfanin ya riga ya gina muhimman kayan aiki da ake buƙata.

Dangote, ya ƙara da cewa wannan aikin zai taimaka wajen samar da man fetur ɗin da Afirka ke buƙata, da kuma rage shigo da mai daga ƙasashen waje.

A cewarsa aikin zai samar da guraben aiki har 65,000, inda kashi 85 cikin 100 na ma’aikatan za su kasance ’yan Najeriya.

“Manufarmu ita ce mu samar da guraben aiki da horar mutanenmu,” in ji shi.

Dangote, ya kuma sanar da cewa matatar za ta kasance a kasuwar hannun jari ta Najeriya a shekarar 2026, domin ’yan Najeriya su samu damar siyan hannayen jari.

“Muna so kowane ɗan Najeriya ya mallaki wani ɓangare na wannan matatar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa za ake biyan kuɗin aikin daga ribar da kamfanin ke samu, tare da taimakon wasu manyan masu saka hannun jari.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar kula da masu bukata ta musamman a jihar Jigawa za ta gudanar da aikin gyaran gidajen gajiyayyu na shiyyar Birnin Kudu da Gumel a sabuwar shekara.

Shugaban hukumar, Malam Sale Zakar Kafin Hausa, ya bayyana haka lokacin kare kiyasin kasafin kudin 2026 a gaban kwamatin harkokin mata na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Ya ce gidan gajiyayyu na shiyyar Birniwa yana cikin kyakkyawan yanayi da kulawa sosai ta fuskar abinci da sutura da kayan wanka da na wanki da sauran bukatun rayuwa, dan haka gwamnati ta kuduri niyyar gyara sauran gidajen gajiyayyun domin kyautata yanayinsu.

Malam Sale Zakar ya ce an Kara yawan mata masu juna biyu da masu shayarwa da ke amfana da Shirin kula da lafiyar iyali daga 20 zuwa 30 a mazabun jihar 287.

Ya kara da cewa za kuma a kara yawan masu amfana da tallafin masu bukata ta musamman daga 150 zuwa 200 a kowacce karamar hukuma, inda masu bukata ta musamman 540 ke samun tallafin naira 10, 000 a duk wata.

A nasa jawabin shugaban kwamatin harkokin mata na majalisar dokokin jihar Jigawa kuma wakilin mazabar Birnin Kudu Alhaji Muhammad Kabiru Ibrahim ya bayyana gamsuwa da tanade tanaden da aka yiwa mata da yara da tsoffi da marasa galihu da mata masu juna biyu da masu shayarwa da nakasassu.

Ya kuma yi addua’ar Allah Ya sa kasafin kudin ya yi tasiri wajen inganta rayuwar masu karamin karfi da marasa galihu a sabuwar shekara.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
  • Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim