Aminiya:
2025-10-26@22:42:43 GMT

Dangote na shirin faɗaɗa matatarsa don zama mafi girma a duniya

Published: 26th, October 2025 GMT

Alhaji Aliko Dangote, na shirin faɗaɗa matatar mansa domin ta riƙa tace gangar mai miliyan 1.4 a kowace rana.

A halin yanzu, matatar tana tace gangar mai 650,000 a rana, amma Dangote, ya bayyana cewa suna shirin ƙara adadin cikin shekaru uku masu zuwa.

Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki El-Clasico: Real Madrid ta doke Barcelona da ci 2

Ya bayyana haka ne yayin wani taro da manema labarai a ranar Lahadi, inda ya ce faɗaɗa aikin zai sa matatar ta zama mafi girma a duniya.

“Wannan shiri yana nuna yadda muke da cikakken shiri a Afirka da kuma dogaro da makomar Najeriya a ƙarƙashin shugabancin Bola Tinubu,” in ji shi.

Ya bayyana cewa aikin zai gudana cikin sauƙi saboda kamfanin ya riga ya gina muhimman kayan aiki da ake buƙata.

Dangote, ya ƙara da cewa wannan aikin zai taimaka wajen samar da man fetur ɗin da Afirka ke buƙata, da kuma rage shigo da mai daga ƙasashen waje.

A cewarsa aikin zai samar da guraben aiki har 65,000, inda kashi 85 cikin 100 na ma’aikatan za su kasance ’yan Najeriya.

“Manufarmu ita ce mu samar da guraben aiki da horar mutanenmu,” in ji shi.

Dangote, ya kuma sanar da cewa matatar za ta kasance a kasuwar hannun jari ta Najeriya a shekarar 2026, domin ’yan Najeriya su samu damar siyan hannayen jari.

“Muna so kowane ɗan Najeriya ya mallaki wani ɓangare na wannan matatar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa za ake biyan kuɗin aikin daga ribar da kamfanin ke samu, tare da taimakon wasu manyan masu saka hannun jari.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

Gwamna Raɗɗa ya ƙara da cewa wannan zaman sulhu da ɓarayin daji da ake yi al’umma ce take yi ba wai gwamnati ba, ita gwamnati tana iya yin sulhu da ɗan bindigar da ya tuba ya yarda da zaman lafiya kuma ya ajiye mukaminsa.

A cewarsa, rawar da gwamnati take iya takawa shi ne, ta ƙarfafa zaman lafiya, sannan ta tabbatar an bi doka da oda a cikin al’umma. Ya ce abubuwa da gwamnati ke lura da su shi ne, al’umma ta mori zaman lafiya domin bunƙasar tattalin arziki da sauran su. 

Tunda farko a jawabinsa, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Hon. Nasiru Mu’azu Danmusa ya bayyana cewa Gwamna Raɗɗa ya rage ƙarfin harkokin rashin tsaro a Jihar Katsina.

Haka kuma ya bayyana cewa wannan ne karo na uku da aka ƙaddamar da bikin yaye dakarun tsaro na Malam Dikko Raɗɗa, sannan za a sake ƙaddamar da sauran a watan Nuwambar wannan shekarar idan Allah ya kai mu rai da lafiya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri October 24, 2025 Labarai Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe October 24, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya October 24, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
  • Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya
  • Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%
  • Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya
  • Farfesa Muhammed Khalid Othman Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Ta Dutsinma
  • Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
  • Shugaba Tinubu Ya Jaddada Kudurin Gwamnatinsa Na Ƙara Zuba Jari A Ilimi
  • NAJERIYA A YAU: Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas?