Dangote na shirin faɗaɗa matatarsa don zama mafi girma a duniya
Published: 26th, October 2025 GMT
Alhaji Aliko Dangote, na shirin faɗaɗa matatar mansa domin ta riƙa tace gangar mai miliyan 1.4 a kowace rana.
A halin yanzu, matatar tana tace gangar mai 650,000 a rana, amma Dangote, ya bayyana cewa suna shirin ƙara adadin cikin shekaru uku masu zuwa.
Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki El-Clasico: Real Madrid ta doke Barcelona da ci 2Ya bayyana haka ne yayin wani taro da manema labarai a ranar Lahadi, inda ya ce faɗaɗa aikin zai sa matatar ta zama mafi girma a duniya.
“Wannan shiri yana nuna yadda muke da cikakken shiri a Afirka da kuma dogaro da makomar Najeriya a ƙarƙashin shugabancin Bola Tinubu,” in ji shi.
Ya bayyana cewa aikin zai gudana cikin sauƙi saboda kamfanin ya riga ya gina muhimman kayan aiki da ake buƙata.
Dangote, ya ƙara da cewa wannan aikin zai taimaka wajen samar da man fetur ɗin da Afirka ke buƙata, da kuma rage shigo da mai daga ƙasashen waje.
A cewarsa aikin zai samar da guraben aiki har 65,000, inda kashi 85 cikin 100 na ma’aikatan za su kasance ’yan Najeriya.
“Manufarmu ita ce mu samar da guraben aiki da horar mutanenmu,” in ji shi.
Dangote, ya kuma sanar da cewa matatar za ta kasance a kasuwar hannun jari ta Najeriya a shekarar 2026, domin ’yan Najeriya su samu damar siyan hannayen jari.
“Muna so kowane ɗan Najeriya ya mallaki wani ɓangare na wannan matatar,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa za ake biyan kuɗin aikin daga ribar da kamfanin ke samu, tare da taimakon wasu manyan masu saka hannun jari.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
Gwamna Raɗɗa ya ƙara da cewa wannan zaman sulhu da ɓarayin daji da ake yi al’umma ce take yi ba wai gwamnati ba, ita gwamnati tana iya yin sulhu da ɗan bindigar da ya tuba ya yarda da zaman lafiya kuma ya ajiye mukaminsa.
A cewarsa, rawar da gwamnati take iya takawa shi ne, ta ƙarfafa zaman lafiya, sannan ta tabbatar an bi doka da oda a cikin al’umma. Ya ce abubuwa da gwamnati ke lura da su shi ne, al’umma ta mori zaman lafiya domin bunƙasar tattalin arziki da sauran su.
Tunda farko a jawabinsa, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Hon. Nasiru Mu’azu Danmusa ya bayyana cewa Gwamna Raɗɗa ya rage ƙarfin harkokin rashin tsaro a Jihar Katsina.
Haka kuma ya bayyana cewa wannan ne karo na uku da aka ƙaddamar da bikin yaye dakarun tsaro na Malam Dikko Raɗɗa, sannan za a sake ƙaddamar da sauran a watan Nuwambar wannan shekarar idan Allah ya kai mu rai da lafiya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA