Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
Published: 26th, October 2025 GMT
Waɗannan matsalolin, sun sanya ake yin jigilar kayan ta kan hanya, a manyan motoci, wanda hakan ya sanya masu ruwa da tsaki a fannin ke ci gaba da kokawa, saboda kuɗaɗen da suke kashewa masu yawa, wajen jigilar kayansu
wanda hakan ya saɓawa manufar ta kafa Tashodhin Jiragen Ruwan ta kantudu.
Injiniya Kayode Opeifa Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ƙasa na ƙasa ya tabbatar da waɗannan matsalolin a taron 2025 Ƙungiyar ‘Yan Jarida Wakilai da ke ɗauko rahotannin ɓangaren sufuri TCAN, da aka gudanar a jihar Legas.
A cewar Kayode, ƙalubalen rashin tsaro, a jihar Neja, hakan ya tilasta Hukumar dakatar da jigilar kayan ta hanyar amfani da Jirgin ƙasa zuwa Kaduna.
Sai dai ya bayyana cewa gwamnonin jihohin Neja da Kaduna, sun yi haɗaka domin lalubo da mafita kan lamarin.
Wani Babban Jami’i a Tashar ta kantudu da ke a jihar Kaduna wanda bai buƙaci a sakaya sunansa ya shedawa LEADERSHIP cewa, baya ga ƙalubalen rashin tsaro, ambaliyar ruwan sama da ta auku a jihar Nije, ta janyo yin gaba da wasu ƙarafan da Jirgin ƙasa ke bi, wanda hakan ya dates ɗaukacin duk wata zirga-zirgar Jiragen zuwa Tashar.
“Muna ci ga da jiran Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ƙasa ta ƙasa NRC, domin ta gyran hanyar ta layin Dogon, wanda kuma idan harkar tsaro ta ƙaru, hakan zai bai wa masu hada-hadar safarar kaya a Jiragen Ƙasan, su samu damar ci gaba da yi zuwa Tashar ta Kantudu, da ke a jihar ta Kaduna, “ A cewar babban jami’i.
Ya ƙara da cewa, yayin da ayyukan sufurin suka tsaya tska, hakan ya sanya ba a yin safarar kaya a cikin Jiragen zuwa Tashar.
Sai dai, wasu masu ruwa da tsaki a fannin sun bayyana fargabar da cewa, ci gaba da ɓata lokaci da ake yi na rashin yin amfani da Tashar hakan zai karya masu ƙwaiwa na ci gaba da yin amfani da Tashar wajen yin safarar kayansu zuwa Tashar.
Bugu da ƙari, sun bayyana cewa, hakan zai kuma mayar da hannun Agogo bayan na ƙiƙarin Gwamnatin Tarayya na ci gaba da ɗaga darajar Tashoshin na Kandu, da aka samar a ƙasar, musamman wajen samar da sauƙin gudanar da hada-hadar kasuwanci a yankin Afirka.
Sai dai, duk da wannan ƙalubalen Hukumar ta NRC da kuma sauran gwamnonin jihohin da abin ya shafa, na kan yin aiki daomin sake dawo da zirga-ziragar kaya zuwa Tashar ta hanyar ƙara ƙarfafa tasaro da kuma sanya wasu ƙarafan na layin Dogo, da ambaliar ruwan saman, ta yi gaba da su.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: zuwa Tashar
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba, ya umarci a gaggawata gyaran bututun da suka hada tashar tacewa da samar da ruwa yankunan Dutsawa da Kantudu.
Wannan mataki ya biyo bayan matsalolin da ake yawan fuskanta sakamakon lalacewar wutar lantarki da na’urar janareto, wanda ke hana jama’a samun ruwa yadda ya kamata.
Yayin da yake bayyana jimaminsa bisa wannan lamari, Dr. Muhammad Uba ya basu tabbacin cewa In Shaa Allahu matsalar ta zo karshe.
A cewarsa, majalisar ta kudirin aniyar yin duk mai yiwuwa domin magance matsalolin da ake fuskanta tare da tabbatar da samun isasshen tsaftataccen ruwan sha ga al’umma.
Ya yi alkawarin tura dukkan kayan aiki da ake bukata domin ganin an warware matsalar.
Dr. Muhammad Uba ya kuma bukaci ma’aikatan hukumar ruwa ta Birnin Kudu da su kara jajircewa wajen kula da tsarin domin kauce wa sake fuskantar irin wannan matsala a gaba.
“Ina karfafa gwiwar dukkan ma’aikatan hukumar ruwa da su kasance masu lura, su zama masu saurin daukar mataki, kuma su kawar da duk wani cikas da zai hana cimma burin samar da ruwa mai dorewa a ko’ina cikin Birnin Kudu.”
Shugaban ya bayyana cewa aikin da ake yi a babbar tashar tacewa da samar da ruwan sha ya kusa kammaluwa.
A cewarsa, wannan aikin tare da gyaran bututun da ake yi yanzu na daga cikin babban shirin gwamnatinsa na inganta samar da ruwa a fadin karamar hukumar.
Wasu daga cikin mutanen yankin sun ce wannan mataki ya nuna jajircewar Dr. Uba wajen inganta muhimman ababen more rayuwa da kuma kyautata jin dadin al’ummar Birnin Kudu.