Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna
Published: 30th, October 2025 GMT
Daga Abdullahi Shettima.
Ƙungiyar taimako mai zaman kanta mai suna Rays Heaven for Special Needs Children and Adults ta gudanar da taron wayar da kai a Kaduna domin ƙarfafa fahimtar muhimmancin kula da lafiyar kwakwalwa da kuma magance matsalolin tattalin arziki da ke shafar rukunin jama’a masu rauni.
Shugaban shirye-shiryen ƙungiyar, Sadiq Abdilatif, ya bayyana cewa wannan shiri mai taken Youth Resilience Project ana aiwatar da shi ne da tallafin Ƙungiyar Tarayyar Turai (European Union) tare da Global Youth Mobilization Fund.
Ya ce manufar shirin ita ce wayar da kai ga makarantun sakandare, al’ummomi, da sansanonin ’yan gudun hijira kan mahimmancin lafiyar kwakwalwa, tare da ƙarfafa matasa su koyi magana idan suna fuskantar damuwa ko matsaloli, da kuma koyar da malamai da shugabannin al’umma hanyoyin taimaka musu.
Mr. Abdilatif ya bayyana cewa matasa da mutane masu buƙata ta musamman, ciki har da ’yan gudun hijira, na fama da ƙalubalen tunani da na tattalin arziki da ke rage musu ƙarfi wajen gudanar da rayuwa. Ya ce wannan shiri yana nufin gina ƙarfin gwiwa da samar da wakilai a cikin al’umma waɗanda za su ci gaba da yada wannan saƙo a yankunansu.
Ya ƙara da cewa ƙungiyar na da shirin haɗa shugabannin gargajiya da na addini domin tabbatar da ci gaba da wayar da kai a matakin ƙasa, yana mai cewa batun lafiyar kwakwalwa abin ne da ya shafi kowa.
Ɗaya daga cikin mahalarta shirin, Salma Hussaini, wadda ba ta da gani, ta yaba da yadda ƙungiyar ta haɗa masu buƙata ta musamman a cikin shirin. Ta ce ta amfana sosai wajen fahimtar yadda ƙarfin tunani da dogaro da kai ke taimakawa mutum ya shawo kan ƙalubalen da yake fuskanta duk da rashin lafiyar jiki.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwakwalwa Ƙungiya Lafiya Rays Heaven Wayar da Kai
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin ADC: Sanata Nenadi ta zama shugaba a Kaduna
Rikicin Jam’iyyar ADC na Jihar Kaduna ya ɗauki sabon salo, bayan da uwar jam’iyyar ta nada tsohuwar Ministar Kuɗi, Sanata Nenadi Usman, a matsayin Shugabar Hadakar Jam’iyyar a jihar.
Haka kuma jam’iyyar ta nada tsohon Kwamishinan Kudi na Jihar Kaduna, Bashir Sa’idu, na hannun daman tsohon gwamnan jihar, Mallam Nasir El-Rufa’i, a matsayin Mataimakin Shugaban Haɗakar.
Da yake jawabi yayin taron manema labarai, Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na Kasa (Arewa maso Yamma), Ja’afaru Sani, ya bayyana cewa manufar ADC ita ce haɗa kan shugabannin jam’iyyun adawa a Kaduna domin ƙarfafa dimokuradiyya da shigar kowa cikin harkokin siyasa.
Ya ce shugabannin Haɗakar sun ƙuduri aniyar sake farfaɗo da jam’iyyar da kuma haɗa kan jama’a don kawo ƙarshen abin da ya kira “mulkin danniya na Jam’iyyar APC a jihar da ƙasa baki ɗaya.”
Tinubu ya gana da sabbin hafsoshin tsaro Alassane Ouattara ya lashe zaɓen Ivory Coast karo na huɗu“A bisa wannan tsari na sake gina jam’iyyar da samar da shugabanci mai tsari, mun tabbatar da naɗin Sanata Nenadi Usman a matsayin Shugabar Hadakar ADC a Jihar Kaduna, tare da Alhaji Bashir Sa’idu a matsayin Mataimakinta.
“Da wannan mataki, ita ce za ta zama ginshiƙin hada kai da shirya ayyukan Haɗakar jam’iyyar a jihar,” in ji shi.
Ja’afaru Sani ya zargi jam’iyyar APC mai mulki da ƙoƙarin raba kawunan shugabannin jam’iyyun adawa a jihar, amma ya ce ADC za ta tsaya tsayin daka wajen kare haɗin kanta.
“Mun lura cewa a ƙoƙarinsu na kawo rabuwar kai, wasu ’yan siyasa da ake amfani da su sun ɗauki nauyin wasu mutane don kai ƙara kotu a kan wasu shugabannin Haɗakar, ciki har da Mallam Nasir El-Rufa’i da ni kaina,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, shugabannin Haɗakar sun cimma matsaya ɗaya ta kora da hana shiga ayyukan jam’iyya ga dukkan mambobin da ke da hannu ƙarar da aka shigar a kotu kan El-Rufa’i da sauran shugabannin jam’iyyar.