Aminiya:
2025-12-12@15:50:47 GMT

Jami’an tsaro sun kashe ’yan bindiga 80 a Kebbi

Published: 28th, October 2025 GMT

Jami’an tsaron hadin gwiwar sun kashe fiye da ’yan bindiga 80 da suka yi yunƙurin kutsawa Jihar Kebbi ta iyakarta da Zamfara.

Rahotanni sun bayyana cewa, sojojin sama da na ƙasa sun gudanar da sumame a dajin Makuku, inda suka yi ruwan wuta kan sansanonin ’yan ta’adda, suka kuma kashe da dama daga cikinsu.

Dakarun sun kuma ceto mutane biyu da ’yan bindigar suka yi garkuwa da su.

A wata sanarwa da Daraktan Tsaro na Ofishin Majalisar Zartarwa ta Jihar Kebbi, Abdulrahman Zagga, ya fitar, an bayyana cewa dakarun sun yi nasarar daƙile wani mummunan hari da sama da ’yan bindiga 400 suka kai garin Ribah, inda aka yi musu mummunar ɓarna.

An kashe wasu makiyaya 10 a Kebbi Rikicin ADC: Sanata Nenadi ta zama shugaba a Kaduna

Mai ba Gwamnan Jihar Kebbi shawara kan harkokin sadarwa da dabarun mulki, Abdullahi Idris Zuru, ya shaida wa manema labarai, cewa wannan aiki ya nuna tsayin daka da ƙarfin dakarun tsaro wajen yaƙi da ’yan ta’adda.

Ya ce, “Dakarun sun yi aiki tuƙuru don hana ’yan bindigar kutsawa cikin Kebbi. Wannan sumame wani ɓangare ne na ci gaba da ƙoƙarin daƙile ta’addanci da fashi da makami a fadin jihar.

“Sojojin Najeriya suna ci gaba da kai hare-hare a dazuka da yankunan da ke kan iyaka, musamman a dajin Makuku.”

Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar tana aiki kafaɗa-da-kafaɗa da hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayukan jama’a da dukiyoyinsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jami an Tsaro Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro

A nan za mu iya cewa, wannan zunzurutun kudaden da za su tara har Naira biliyan 19 a wata daya, ya zama wajibi alummar yankin su sauya, na dakile matsalar domin kuwa, ‘yan Nijeriya, sun gaji batun ana tara dimbin kudade, domin magance wata matsala a kasar, amma daga, a karkatar da su, zuwa wata sabga, ta da ban.

Kazalika, batun ba wai kawai na tara wadannan zunzurutun kudaden ba ne, amma babbar ahaure’yan ambayar a nan ita ce, shin wa zai tafiyar da wadanda kudaden ? kuma shin, takamai-mai, wacce daga cikin matsalar ta tsaron, za a tunkarar? ta yaya za a kashe kudaden tare da fayyace yadda aka kashe su?

Matukar gwamonin, ba su bayar da wata gamsasshiyar amsar wadannan tamaboyin ba, wannan Gidauniyar, za ta kasance a cikin shakku, wadda za ta kasance wata hanya ta arzurta ‘yan Kwangila da kuma wasu da za a dauko, a matsayin mutanen tuntba, inda su kuma alumomin da ya kamata, magance masu kalubalen, za su ci gaba kai Gawarwakin ‘yanuwansu, makabartu, suna bizne su, saboda ci gaba da hare-haren na ‘yan bindiga.

Bugu da kari, Gwamonin sun bukaci da a dakatar da hakar ma’adanai, har na tsawon watanni shida, duba da cewa, hakar na’adanan, ta haramtacciyar hanyar, ta kasance tamkar wata hanya, samun kudaden ga ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda.

Alumomin da ke a jihohin Zamfara, Kaduna da Neja, sun ci gaba da fuskantar ‘yan bindiga da kuma’yan ta’adda bakin haure, ke kutsawa cikin alumomin da ke a wadannan jihohin suna hana su, kwanciyar hankali, tare da gindaya masu haraji.

A yanzu, Gwamonin na son ganin an tsaftace fannin na hakar ma’adanai ta hayar bayar da lasisi.

A nan, za a iya cewa, dakatawar ta watanni shida, ba ta wadatar ba, domin har yanzu, wasu na ci gaba da gudanar da ayyukan, ta haramtacciyar hanya.

A saboda haka, ya zama wajibi Gwamonin, su bukaci Ma’aikatar Hakar Ma’adanai ta Tarayya da ta sanar da su, ainahin kamfanonin da suka mallaki lasisin hakar ma’adanai tare da kuma wadanda suke amfana da fannin.

Hakazalika, akwai bukatar jihohin su samu cikakkun bayanan sirri, kan ayyukan da a ke gudanarwa, ba hakar ma’adanai a jihohin su da alumomin da abin ya shafa, inda kuma alummar, na ‘yancin su fada ko har yanzu, ana ci gaba da gudanar da ayyukan a yankunan su.

Kazalika, gungiyay ta kuma goyi bayan kafa ‘yansanda na jihohi, inda shi kasansa, wannan batun ke da bukatar, a yi dogon nazari a kai.

A bisa tunaninsu, kirkiro da ‘yansandan na jihohi, ita ce, hanya daya tilo, za a iya magance kalubalen rashin tsaro

Abu daya da takardar sakamakon taron ba su ta tsalle shi ne, shin a ta yaya ne, yankin ya tsinci kasansa, a cikin wannan matsalar ta rashin tsaro.

Gwamonin su kuma mika ta’aziyyarsu ga shugaba Bola Tinubu da kuma kokarin da yake ci gaba da yi, na tabbatar da tsaro, amma sun gaza yin dubi ga batun cin hanci da rashawa da yin tunani kan yadda ‘yan bindiga da kuma’yan ta’adda, ke ci gaba da aikata ta’asarsu, a cikin alumomi ba.

A nan za mu iya cwa, batun ya fi karfin tara kudade da damar da kayan aiki, amma dole ne, Gwamnonin su fuskanci gaskiya, musamman kan gazawar iya shugabanci wadda ta bayar da damar samun matsalar ta rashin tsaro.

Ya zama wajibi, Gwamnonin su yi dubi kan yadda ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda ke watayawarsu a cikin alumma tare da kakkafa sansanoninsu su kuma kai hare-harensu, ba tare da a far masu ba.

Batun na tara Naira biliyan 228 a shekara, batu ne da ya wuce maganar fitar da sanarwa ga kafafen yada labarai, amma sakamko na gari, shi ne ake bukata.

Shin dalibai a jihar Zamfara, za su iya zuwa makarantunsu na Boko, ba tare da jin wani tsoro ba? Manoma a jihar Kaduna, za su iya zuwa su iya komawa ci gaba da noma gonaksnu ba tare da wata fargaba ba? Matafiya za su iya bin babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna ba tare da ‘yan bindiga sun kai masu hari ba?

Gwamnonin sun dauki matakai da dabaru na zuba kudade domin tunkarar kalubalen na rashin tsaro.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara December 11, 2025 Manyan Labarai EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Anambra Chris Ngige A Abuja December 11, 2025 Manyan Labarai Rikicin PDP Ne Ya Sanya Ni Komawa Jam’iyyar Accord – Adeleke December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji