Leadership News Hausa:
2025-10-25@23:28:05 GMT

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Published: 26th, October 2025 GMT

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan kasar Sin Li Qiang ya isa Singapore a yau Asabar don ziyarar aiki a kasar bisa gayyatar firaministan Singapore Lawrence Wong.

Li ya bayyana cewa, a cikin shekaru 35 da suka gabata tun bayan kafa huldar diflomasiyya, dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu ta ci gaba da kasancewa mai kyau da samun ci gaba, tare da zurfafa amincewa da juna a siyasance, da hadin gwiwa mai amfani da kuma mu’amala ta kut-da-kut tsakanin mutanensu, wanda ya kafa misali don koyo tare da hadin gwiwar samun nasara ga kowane bangare a tsakanin kasashe.

Ya kara da cewa, kasar Sin tana son yin aiki tare da Singapore don karfafa daidaita dabarun ci gaba, da fadada hadin gwiwa mai amfani ga dukkan bangarorin biyu, da ci gaba da yin aiki tare a cikin shirin zamanantarwa, da kuma bayar da gudummawa sosai wajen tabbatar da hadin gwiwa tsakanin bangarori daban-daban da kuma bunkasa ci gaba na bai-daya a yankin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing October 25, 2025 Daga Birnin Sin Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD October 25, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15 October 25, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

Mahalifinsa, Chief Thomas Osen Ekpemupolo, da mahaifiyarsa, Mrs. Ewe Ekpemupolo, sun rayu cikin al’umma mai arziƙin mai a lokacin da ake tsaka da nema a yi wa yankinsu adalci. Daga cikin wannan rikicewar ya taso mutum wanda daga baya zai zama ɗan gwagwarmayar Niger Delta don neman daraja, adalci, da samun ikon gashin kai.

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta Sojoji Sun Lalata Matatun Mai 20 A Yankin Niger Delta

A tsakiyar shekarun 1990, arzikin mai na Nijeriya yana samu wadata a wasu wurare amma ya zama ana barin al’ummomi masu arziƙin mai cikin talauci, gurɓawa, da kuma rashin muryar magana. Ga matashin Tompolo, yin shiru wannan bai zama zaɓi ba.

 

Gwagwarmaya Da Juyin Juya Hali

A Ƙaramar Hukumar Kudu maso Yammacin Warri, daga Ogbe-Ijoh (garin Ijaw) zuwa Ogidigben (garin Itsekiri), an yanke shawarar da ta haifar da tashin hankali na ƙabilanci kuma ta ƙwace ikon alama daga wata ƙabilar baki ɗaya.

Tompolo ya sayar da kusan duk abin da yake da shi, gidaje uku, motar Mercedes Benz Ɓ-Boot, da jiragen ruwa da dama, don samar da kuɗi ga yakin neman gyara wannan rashin adalci. Jarumtarsa ta ja hankalin mutane, tana kuma haifar da tsoro.

A ƙarshe, a ƙarƙashin Shugaba Olusegun Obasanjo, gwamnatin tarayya ta janye shawarar, ta mayar da hedkwatar zuwa Ogbe-Ijoh. Wannan nasara ce ta farko a fili, ba ta tashin hankali ba, ta jajircewa.

A cikin shekarun da suka biyo baya, Tompolo ya fito a matsayin muryar jagoranci a gwagwarmayar Neja Delta. A matsayin wanda ya kafa ‘Moɓement for the Emancipation of the Niger Delta’ (MEND), ya ƙalubalanci tsarin tarayya wanda ke ƙwace biliyoyi daga ƙasar yankin amma ba ya mayar da komai. Saƙonsa yana da sauƙi amma mai ƙarfi ne: “Ba mu nemi yaki ba; muna neman adalci ne.”

Lokacin sauyi ya zo a shekarar 2009, lokacin da ya amince da Shirin Afuwa na Shugaban Ƙasa da marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua ya ƙaddamar. Duk da cin mutuncin wasu da shakku, ya ajiye makamai, yana ƙarfafa wasu su yi haka. Wannan ɗaya daga cikin ayyuka ya taimaka wajen kawo ƙarshen shekaru na tashin hankali da buɗe ƙofa ga gina zaman lafiya da tattaunawa mai tsari. Wannan shi ne farkon sauyi na mutum ɗaya da yankin baki ɗaya.

 

Daga Mai Ta Da Ƙayar Baya Zuwa Mai Tsara Ɗorewar Zaman Lafiya

Hannayen da da suka taɓa jagorantar jiragen yaƙi yanzu suna kula da wani sabon nau’in jiragen ruwa na ƙirƙira, samar da ayyukan yi, da kiyaye zaman lafiya. Ta hanyar Tantita Security Serɓices Nigeria Limited (TSSL), tare da haɗin gwiwa da Nigerian National Petroleum Company Limited (NNPCL), Tompolo ya zama mai tsaron muhimman kadarorin Nijeriya: bututun mai da tashoshin ruwan gabar teku.

Tsarin Tantita ya haɗa tsarin sa ido na zamani da bayanan sirri daga cikin al’umma, wanda hakan ya rage satar mai da aikin tace mai ba bisa ƙa’ida ba (“Kpo-fire”) a faɗin Niger Delta. Waɗannan ƙoƙari sun taimaka wajen ƙara yawan fitar da man fetur na kullum a Nijeriya, haɓaka kuɗaɗen shiga na gwamnati, da kuma dawo da amincewa da tsaron da al’umma ke jagoranta.

Amma ribar tattalin arziki rabin labari ne kawai. Fiye da mutane 3,000 daga cikin tsofaffin masu tayar da ƙayar baya da matasan yankin sun samu aikin doka mai ɗorewa ƙarƙashin kulawar Tantita.

Da yawa daga cikin waɗanda da suka ɗauki tawaye a matsayin hanya ɗaya ta samun muhimmanci, yanzu suna sanye da kayan aikin da ke da ma’ana. A cikin rafukan da da ake jin ƙarar bindigogi, yanzu ana jin ƙarar injinan jiragen ruwa masu ɗaukar ƙungiyoyin masu sa ido — hujja ce cewa zaman lafiya na iya kawo riba.

 

Faruwar Samun Nasarar Jin Ƙai

Nasarar da ta fi kowace girma ga Tompolo ita ce ta aikin jin ƙai cikin natsuwa.

Ta hannun Tompolo Education Foundation, yana ba da tallafin karatu da horas da malamai ga ɗaruruwan ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi a faɗin yankin Neja Delta.

A watan Maris 2025, cibiyar ta ƙaddamar da shiria gina ƙwarewa ga ‘yan NYSC a yankin Warri domin ƙarfafa sababbin malamai da za su koyar a al’ummomin da ba su da wadatattun malamai.

Lokacin da Jami’ar Kiwon Ruwa ta Nijeriya (Nigeria Maritime Uniɓersity), Okerenkoko, ta gudanar da bikin yaye ɗalibai na farko, Tompolo ta hannun cibiyarsa ya ba da kayan ɗaki masu darajar Naira miliyan 30 don ƙarfafa muhalli na koyo.

Wannan ba taimako kawai ba ne, wani yanayi ne da ya tabbata: Tompolo ɗin da a da ake kira ɗan tawaye, yanzu shi ne ke zuba jari a cikin sabunta ilimin zamani.

 

Jin Ƙaunarsa Ta Kai Har Ga Fannin Kiwon Lafiya

A shekara ta 2012, ya biya kuɗin gyaran asibitin Okerenkoko guda ɗaya da darajar kuɗin suka kai naira miliyan 20.

Haka kuma, yayin ambaliyar ruwa ta shekarar 2022, Tompolo ya ba da kayan tallafi na darajar ta kai Naira miliyan 150 ga waɗanda ambaliyar ta shafa a jihohin Bayelsa da Delta, da Riɓers.

A gefe guda, Cibiyar Al’adu ta Izon (Izon Cultural Heritage Centre – ICHC) da Ƙungiyar Ayyukan Al’umma ta Izon (Izon Community Serɓice Ɓolunteers – ICSƁ) sun zama tushen farfaɗo da al’adu da ƙarfafa hidima ga al’umma.

Ta hanyar waɗannan ƙungiyoyi, Tompolo yana tunatar da matasan Ijaw cewa hidima ita ce mafi muhimmanci, kuma asalin bayyana kai ba wani tsohon abu ba ne tushen rayuwa ne mai ƙarfi da ci gaba.

 

Girmamawa Daga Jami’ar Maritime

Sauyin da ya samu daga kasancewa kwamandan ’yan tawaye zuwa zama mai daidaita ƙasa ya jawo masa yabo daga ko’ina.

A shekarar 2023, Jami’ar Maritime ta Nijeriya  ta ba shi digirin girmamawa saboda gudunmawar da ya bayar wajen samar da zaman lafiya da ci gaba.

A shekara ta gaba kuma, Ƙungiyar Mutanen Ijaw ta Birtaniya da Ireland (Ijaw People’s Association – IPA) ta ba shi kyautar “Izon-Ebi Dou Keme” wato “Jagora mai kishin ci gaban al’ummar Ijaw.”

A yayin bikin ba da lambar girmamawar, Francis Akpanari, shugaban IPA, ya bayyana shi a matsayin “halattaccen ɗan Ijaw, wanda ya zama wata gada tsakanin rikici da haɗin kai.”

Amma wataƙila gaskatacciyar girmamawa ta fito ne daga al’umma kanta.

A cikin wata buɗaɗɗiyar wasika da ta bazu a kafafen sada zumunta, Oyinke Preye Tales, wata matashiya daga kogunan yankin, ta rubuta da motsin rai:

“Ba kawai shugaba ba ne kai, babban Cif ne kai, ƙarfi ne na yanayi, mai kare mutanen Ijaw da yankin Neja Delta.

Ka tsaya tsayin daka lokacin da da yawa suka durƙusa. Ka ɗauki nauyin fafutukar mu har da haɗarin rayuwa.

Saboda kai, ina tafiya ina ɗaga kai da alfahari.”

Wannan yabo ne na bazata daga sabon ƙarni wanda ba ta ganin yankin Neja Delta a matsayin wurin baƙin ciki da lalacewa, sai dai a matsayin wurin farfaɗo da sabuwar rayuwar abin da aka samu, a wani ɓangare, saboda zabin da ya yi da jagorancin da ya nuna.

 

Rayuwa Tasa, Manufa ta Jama’a

Duk da shahararsa da tasirinsa a siyasa, Tompolo har yanzu yana rayuwa cikin sauƙi da tawali’u. Yana zaune cikin natsuwa a Jihar Delta tare da matarsa Ɓictoria da ’yarsa Mary, yana guje wa nuna isa da shahara, yana fifita tunani da tunawa.

Masu kusanci da shi suna bayyana shi a matsayin mutum mai cike da natsuwa, wanda har yanzu yake ɗauke da raunukan yaƙin da ya shuɗe, amma yana samun warkewa ta hanyar zaman lafiya da ya taimakawa wajen gina al’umma.

A Wajen Mutanensa, Shi Ne Ibe-Ebidouwei Na Al’ummar Ijaw “Wanda Ke Kawo Alheri Ga Jama’a.”

A wajen Nijeriya kuma, shi hujja ce cewa sasantawa ba rauni ba ce, kuma cewa tuba da aka haɗa da manufa na iya zama babban arzikin ƙasa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar October 24, 2025 Manyan Labarai Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri October 24, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya October 24, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa
  • Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba
  • Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu
  • Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu
  • Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
  • Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
  • Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta
  • Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba
  • Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka