Aminiya:
2025-10-29@15:11:17 GMT

An ceto jaririya ’yar mako daya da haihuwa da aka sayar a Anambra

Published: 29th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Anambra ta ce ta ceto wata jaririya da ba ta wuce mako daya da haihuwa ba, da aka sayar kan kuɗi Naira miliyan ɗaya da rabi, tare da cafke mata huɗu da ake zargin su da hannu a cinikin.

Kakakin rundunar a jihar, SP Tochukwu Ikenga, ya shaida wa Aminiya cewa an samu labarin sayar da jaririyar ne a kauyen Ifite-Awkuzu da ke Karamar Hukumar Oti, inda rundunar ta ɗauki matakin gaggawa na cafke waɗanda ake zargin.

An kai ƙarar malamai 2 kan zargin ɓatanci ga Annabi a Kaduna Uwa da ’yarta sun nitse a hatsarin jirgin ruwa a Borno

Waɗanda aka kama sun haɗa da Elizabeth Okafor mai kimanin shekara 62, Esther Nweke mai shekara 48, Ngozi Maanfa mai shekara 45, da Peace Elijah Moses, wadda ita ce mafi ƙarancin shekaru a cikin su, mai kimanin shekara 25.

Ikenga ya ce binciken da rundunar ta gudanar ya tabbatar da cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin sayen jaririyar ba tare da an tursasa su ba, kuma ba a yi masu duka ko azabtarwa ba kafin su bayyana gaskiya.

“Jaririyar tana cikin ƙoshin lafiya, ba ta samu wata matsala ba,” in ji Ikenga.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ikioye Orutugu, ya bayar da umarnin a mika waɗanda ake zargin zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) domin ci gaba da bincike.

Ya ce bayan kammala binciken, za a gurfanar da su a gaban kotu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Anambra Satara jarirai da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

 

Wannan tabbacin ya zo ne a daidai lokacin da farashin famfon mai ke canzawa a faɗin ƙasar, wanda tun daga kusan ₦189 a kowace lita a shekarar 2023 zuwa sama da ₦1,000, kafin ya daidaita tsakanin ₦800 da ₦900 a farkon shekarar 2025.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga  October 27, 2025 Labarai Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa October 27, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno October 27, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duk da ce-ce-ku-ce sunan Maryam Sanda na cikin wadanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • An kai ƙarar malamai 2 kan zargin ɓatanci ga Annabi a Kaduna
  • Gwamnatin Kamaru za ta gurfanar da Issa Tchiroma a kotu kan zargin tayar da zaune tsaye
  • Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra
  • An raba wa iyalan ’yan sandan da suka mutu tallafin N31m a Jigawa
  • Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
  • Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
  • Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 
  • Paul Biya mai shekara 92 ya lashe zaɓen Kamaru