An kama mutum 25 kan zargin shirya auren jinsi a Kano
Published: 26th, October 2025 GMT
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta samu nasarar cafke wasu mutum 25 da ake zargi da shirya auren jinsi a samamen da ta kai wani wurin shagali a jihar.
A cewar hukumar, an kama mutanen ne da yammacin Asabar a wani wurin taro da ke kan titin Hotoro Bypass a ƙaramar hukumar Tarauni.
Sojoji sun daƙile harin ISWAP a Borno NSCDC ta yi alhinin mutuwar Kwamishinan Tsaron GombeMataimakin Kwamanda Janar na Hukumar Hisbah mai kula da ayyuka na musamman, Sheikh Dokta Mujahid Aminuddeen Abubakar, ne ya tabbatar da kama waɗanda ake zargin a ranar Lahadi.
Ya bayyana cewa samamen na zuwa ne bayan bayanan sirri da hukumar ta samu daga wani mai kishin al’umma.
Ya bayyana cewa bayanan sirrin sun nuna cewa wani mai suna Abubakar Idris yana shirin auren wani matashi, lamarin da ya sa jami’an Hisbah suka bazama zuwa wurin da taron ke gudana.
Ya ƙara da cewa daga cikin wadanda aka kama akwai maza 18 da aka bayyana a matsayin ’yan daudu, da kuma mata 7 daga unguwanni daban-daban ciki har da Sheka, Yar Gaya da Kofar Nasarawa.
Dokta Mujahid ya ce a halin yanzu duk ababen zargin suna hannun hukumar, kuma za a gurfanar da su gaban kotu da zarar an kammala bincike.
Ya yi kira ga iyaye da su kula wajen inganta tarbiyyar ’ya’yansu, tare da roƙon jama’a da su rika sanar da hukumar Hisbah ko hukumomin tsaro idan sun ga wani abin da ke da ɗaukar hankali.
Mataimakin kwamandan ya sake jaddada ƙudirin hukumar na ci gaba da tabbatar da ɗabi’a ta gari da kare mutuncin Kano a matsayin jihar da aka sani kan ginshiƙin ladabi da ƙa’idojin addinin Musulunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Karfafa Dangantaka Da NAFDAC
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa zata kara karfafa dankon zumunta da Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa NAFDAC.
Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin da mahukunta hukumar NAFDAC suka ziyarce shi a ofishin sa dake Dutse babban birnin jihar.
Ya bayyana farin cikinsa da ziyayar, inda ya jaddada bukatar aiki tare domin cimma dukkan nasarar da ake bukata a tsakanin hukumomin biyu.
Da yake bayani dangane da shirin da hukumar alhazan take yi, Labbo yace dukkanin shirye-shirye sunyi nisa na rigistar kujerun aikin hajji shekarar 2026.
Yana mai cewar, hukumar NAFDAC tana cikin masu ruwa da tsaki na hukumar jin dadin alhazan jihar.
Alhaji Ahmed Labbo, yayi nuni da cewar akowane lokaci za’a iya bukatar tattauna muhimman bayanai na shirye-shiryen aikin hajji domin bada ta su gudunmuwar.
Tun farko a jawabin sa, sabon Shugaban hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC a jihar jigawa, Alhaji Mansur Muhammad yace makasudin ziyarar shi ne domin gabatarwa gami da neman goyan bayan hukumar jin dadin alhazan ta jihar.
Ya kara da cewar, hukumar tana daga cikin hukumomi dake aiki tare da hukumar NAFDAC musamman a lokacin fara jigilar maniyyata.
Mansur Muhammad yace za su ci gaba da bai wa hukumar cikakken hadin kai da goyan baya a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.
Usman Mohammed Zaria