An raba wa iyalan ’yan sandan da suka mutu tallafin N31m a Jigawa
Published: 28th, October 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jigawa ta raba tallafin Naira miliyan 31 ga iyalan jami’ai 59 da suka rasa rayukansu a bakin aiki.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, inda ya bayyana cewa wannan mataki na nuna irin ɗawainiyar da rundunar ‘yan sandan ke yi wajen kula da jin daɗin jami’anta da iyalansu.
Aminiya ta ruwaito cewa Kwamishinan ‘yan sandan Jigawa, CP Dahiru Muhammad ne ya wakilci Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Adeolu Egbetokun, wajen raba tallafin a ƙarƙashin shirin nan na tallafa wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka mutu a bakin aiki wato Group Life Assurance (GLA) da kuma IGP Family Welfare Scheme.
Da yake miƙa tallafin, CP Dahiru ya bayyana jami’an da suka rasu a matsayin “jarumai da suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma domin tabbatar da zaman lafiya da hadin kan ƙasa.”
Ya ce ba za a taba mantawa da gudummuwarsu ba, yana mai jaddada cewa rundunar za ta ci gaba da tallafa wa iyalansu domin rage raɗaɗin rashinsu.
Ya kuma shawarci iyalan mamatan da aka rabawa tallafin da su yi tattalin kuɗaɗen wajen ci gaban iyalansu.
A nasa jawabin, wanda ya wakilci iyalan waɗanda abin ya shafa, Malam Surajo Shehu, ya miƙa godiya ga Sufeto Janar da kwamishinan ‘yan sanda na Jigawa bisa wannan kulawa da jinƙai da suka nuna, tare da alƙawarin amfani da kuɗaɗen domin karrama jaruman jami’an da suka rasu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda iyalai Jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗalibi ya kashe abokinsa, ya binne shi a rami a Filato
Wani ɗalibin Jami’ar Jos da ke Jihar Filato, ya kashe abokinsa, wanda shi ma ɗalibi ne a jami’ar, sannan ya binne gawarsa a bayan gidansu.
Wanda aka kashe mai suna Peter Mafuyai, ɗalibi ne da ke shekara ta uku a sashen hada-hadar kuɗaɗen banki.
Dangote na shirin faɗaɗa matatarsa don zama mafi girma a duniya Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — DasukiAna zargin Nanpon Timnan da ke ajin shekara ta biyu daga sashen karatun harkar noma, da kashe shi sannan ya binne shi a rami.
Rahotanni sun bayyana cewar ɗaliban abokan juna ne sosai.
An ruwaito sun fita ƙwallon ƙafa, daga nan suka wuce wani waje sannan suka dawo gida.
“Da suka dawo Nanpon ya ɗauko adda. Abokansa da suke zaune tare a cikin gidan suka tambaye shi me zai yi da addar, sai ya ce yana son amfani da ita ne,” in ji wata majiya.
“Bayan haka sai ya sari abokinsa Peter da addar. Sauran abokan suka fara ihu suna tambayar dalilin da ya sa ya yi hakan, amma bai ba su amsa ba. Suka fita neman taimako, amma kafin su dawo, tuni ya binne gawar a bayan gidan.”
’Yan sanda sun riga sun gayyaci sauran abokan don yi musu tambayoyi, kuma ana ci gaba da bincike.
Zuwa yanzu dai babu cikakken bayani kan dalilin da ya sa ya yi kisan, sai dai wata majiya ta ce wataƙila sun sama saɓani.
Sakamakon yajin aikin ASUU da ake yi a jami’ar, babu ɗalibai ya bare a samu cikakken bayani ba.
Da aka tuntuɓi Shugabar riƙon ƙwarya ta Sashen Watsa Labarai na jami’ar, Tongdyen Dachung, ta ce ba za ta iya yin magana kan lamarin ba tukunna, domin tana buƙatar tabbatar da wasu bayanai.
Ita kuwa Shugabar Ƙungiyar Ɗaliban Jami’ar (SUG), Jane Pwajok, ta ce lamarin yana hannun ’yan sanda.
Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan Jihar Filato, Alfred Alabo, bai yi nasara ba, domin ba ya ɗaga waya.