Aminiya:
2025-12-13@20:30:07 GMT

Uwa da ’yarta sun nitse a hatsarin jirgin ruwa a Borno

Published: 29th, October 2025 GMT

Habiba Abubakar mai shekaru 35 da ’yarta Adama mai shekaru 9 sun rasa rayukansu bayan hatsarin jirgin ruwa da ya faru a Karamar Hukumar Hawul da ke Jihar Borno.

Mai magana da yawun Rundunar ’San Sanda ta jihar, Nahum Daso, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar, 26 ga Oktoba, 2025, da misalin ƙarfe 1:15 na rana, yayin da suke komawa gida daga gona.

Gwamnatin Kamaru za ta gurfanar da Issa Tchiroma a kotu kan zargin tayar da zaune tsaye Ba daidai ba ne Tinubu ya ci gaba da ciyo bashi duk da cire tallafin mai – Sanusi

Ya ce, “Sun fito daga gona ne kuma suna ƙoƙarin ketare wani kogi da ke kusa da kauyen Ghung. Amma saboda ƙarfi da saurin ruwan, jirgin ruwan nasu ya kife a wani wuri mai zurfi na kogin.”

A cewarsa, jami’an ’yan sanda tare da masu aikin ceto a yankin daga bisani sun gano gawarwakin su daga cikin kogin.

“Ba a ga wata alama ta tashin hankali a jikin gawarwakin ba. An ɗauki hotuna don adana bayanai kafin a kai su Asibitin Garkida da ke Karamar Hukumar Gumbi a Jihar Adamawa, domin shi ne asibitin da ya fi kusa da su,” in ji Daso.

An mika gawarwakin ga iyalansu don yin jana’izar su bisa tsarin Musulunci.

“A halin yanzu, Sashen Binciken Laifuka na Rundunar ’Yan Sandan jihar da ke Maiduguri ya fara bincike kan lamarin,” in ji Daso.

Aminiya ta ruwaito cewa a watan Satumba an gano gawar wani yaro mai sayar da kaya, wanda ake kyautata zaton ya kai shekaru 12, daga cikin kogin Gamboru da ke unguwar Customs a birnin Maiduguri, babban birnin jihar.

A ’yan watannin nan dai ana samun yawan nitsewar jiragen ruwa musamman a yankin Arewa maso Gabas na ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hatsarin Jirgin Ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano

Ya ce, wanda ake kara ya nema kuma an bashi kudin fansa har Naira miliyan 15 daga iyalan wanda aka kashe kafin su kashe shi.

 

“Sun bugi wanda aka kashe a kai da ƙirji da sanda sannan daga baya suka binne gawar a gidan Adamu da ke Dawakin Kudu,” in ji mai gabatar da kara ga kotun.

 

Da take yanke hukunci, Mai Shari’a Aisha Mahmoud ta ce masu gabatar da kara sun tabbatar da hujjoji game da karar da suka shigar a kan Adamu ba tare da wata shakka ba.

 

“Ina yanke wa Adamu hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda ya buga wa wanda aka kashe sanda a kansa da ƙirjinsa, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa. Ubangiji ya yi masa rahama,” in ji ta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II December 11, 2025 Labarai Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto December 11, 2025 Manyan Labarai Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota