Aminiya:
2025-10-27@21:29:27 GMT

An kashe wasu makiyaya 10 a Kebbi

Published: 27th, October 2025 GMT

Aƙalla makiyaya goma aka kashe a wani hari da aka kai wa Fulani makiyaya a wata ruga da ke yankin Tilli a ƙaramar hukumar Bunza ta Jihar Kebbi.

Majiyarmu ta ce harin wanda ya yi kama da na ramuwar gayya na zuwa ne bayan kashe wani ɗan sa-kai a yankin.

An rufe makarantu saboda ƙarancin man fetur a Mali Zanga-zanga ta ɓarke a Kamaru

Bayanai sun ce mutuwar ɗan sa-kan ce ta jawo zargin cewa Fulani ne suka yi kisan, lamarin da ya sa wasu matasa suka dunguma suka kai farmaki a sansanin Fulani, inda suka kashe mutum goma a yayin harin.

Wani mazaunin yankin da ya zanta da wakilinmu ya ce, “kuskuren fahimta ce ta sa aka kai harin.

“Sun ɗauka cewa Fulani ne suka kashe ɗan sa-kan, sai suka kai musu hari a sansaninsu.

“Mutum sama da goma aka kashe, har yanzu ma suna ci gaba da neman wasu da ba a gani ba.”

Majiyar ta ƙara da cewa, Shugaban Ƙasa na ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) tare da Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Umar Tafida, sun ziyarci yankin domin jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa.

Da aka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Nafiu Abubakar, ya ce bai samu labarin lamarin ba a lokacin, amma ya yi alƙawarin binciko gaskiyar abin da ya faru.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, bai waiwayi wakilinmu ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi Makiyaya

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

Yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke shirin tafiya kasar Koriya ta Kudu, domin halartar kwarya-kwaryar taron shugabanni karo na 32, na kungiyar hadin-gwiwar tattalin arzikin kasashen yankin Asiya da Pasifik wato APEC, tare da gudanar da ziyarar aiki a kasar, an gudanar da wani taron tattaunawa, mai taken “Shugabancin duniya da samun wadata tare a yankin Asiya da Pasifik” a nan birnin Beijing, wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG, da jami’ar Yonsei  da gidan talabijin na YTN na Koriya ta Kudu suka shirya tare.

 

Yayin taron, shugaban CMG Shen Haixiong, ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo, inda ya ce “CMG na fatan yin hadin gwiwa mai zurfi tare da kasashen yankin Asiya da Pasifik, don haka ya dace mu ba da labaran hadin gwiwa tare, mu kirkira, kuma mu bunkasa musayar al’adu, mu shiga tattaunawa da hadin gwiwa, sannan mu ba da gudummawar hikimomi da karfinmu, wajen kyautata tsarin shugabancin duniya”. (Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai October 26, 2025 Daga Birnin Sin Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya October 26, 2025 Daga Birnin Sin An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan October 25, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Alassane Ouattara ya lashe zaɓen Ivory Coast karo na huɗu
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe ‘Yan kasar Lebanon Biyu Tare Da Jikkatan Wasu Biyu Na Daban
  • Ɗalibi ya kashe abokinsa, ya binne gawarsa a rami a Filato
  • Ɗalibi ya kashe abokinsa, ya binne shi a rami a Filato
  • Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai
  • An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing
  • Sojoji sun daƙile harin ISWAP a Borno
  • An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
  • ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam