An kashe wasu makiyaya 10 a Kebbi
Published: 27th, October 2025 GMT
Aƙalla makiyaya goma aka kashe a wani hari da aka kai wa Fulani makiyaya a wata ruga da ke yankin Tilli a ƙaramar hukumar Bunza ta Jihar Kebbi.
Majiyarmu ta ce harin wanda ya yi kama da na ramuwar gayya na zuwa ne bayan kashe wani ɗan sa-kai a yankin.
An rufe makarantu saboda ƙarancin man fetur a Mali Zanga-zanga ta ɓarke a KamaruBayanai sun ce mutuwar ɗan sa-kan ce ta jawo zargin cewa Fulani ne suka yi kisan, lamarin da ya sa wasu matasa suka dunguma suka kai farmaki a sansanin Fulani, inda suka kashe mutum goma a yayin harin.
Wani mazaunin yankin da ya zanta da wakilinmu ya ce, “kuskuren fahimta ce ta sa aka kai harin.
“Sun ɗauka cewa Fulani ne suka kashe ɗan sa-kan, sai suka kai musu hari a sansaninsu.
“Mutum sama da goma aka kashe, har yanzu ma suna ci gaba da neman wasu da ba a gani ba.”
Majiyar ta ƙara da cewa, Shugaban Ƙasa na ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) tare da Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Umar Tafida, sun ziyarci yankin domin jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa.
Da aka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Nafiu Abubakar, ya ce bai samu labarin lamarin ba a lokacin, amma ya yi alƙawarin binciko gaskiyar abin da ya faru.
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, bai waiwayi wakilinmu ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi Makiyaya
এছাড়াও পড়ুন:
RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
Kungiyar ‘yan jarida marar iyaka ta RSF, ta fitar da rahoton na shekara shekara wanda a cikinsa ta bayyana cewa, ‘yan jarida 67 suka rasa rayukansu a lokacin da suke bakin aiki ko kuma sakamakon aikinsu a duk duniya,
Saidai a cewar rahoton kusan rabinsu sun mutu a Zirin Gaza, “a lokacin da sojojin Isra’ila suka bude musu wuta.
A cewar rahoton na 2025, “Yawan ‘yan jarida da aka kashe (daga 1 ga Disamba, 2024, zuwa 1 ga Disamba, 2025) ya sake karuwa, saboda laifukan da sojoji masu dauke da makamai na yau da kullun da kuma laifukan da aka tsara.”
Kungiyar ta kuma bayar da rahoton ‘yan jarida 135 da suka ɓace, wasu fiye da shekaru 30, da kuma ‘yan jarida 20 da aka yi garkuwa da su.
‘Yan jaridar Reporters Without Borders sun ƙidaya ‘yan jarida 49 da aka kashe a shekarar 2023, ɗaya daga cikin mafi ƙarancin adadi a cikin shekaru ashirin da suka gabata, amma yaƙin kisan kare dangi da Isra’ila ta yi a zirin Gaza tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023, ya haifar da ƙaruwar wannan adadin a shekarar 2024 (an kashe 66 bisa ga sabuwar ƙidayar da aka yi) da kuma (67) 2025.
Wannan babban kalubale ne ga aikin jarida in ji darektar kungiyar ta RSF Anne Bocandé ga AFP.
Ta kuma bukaci gwamnatoci su sake saka hannun jari don kare ‘yan jarida ba wai, akasin haka ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda December 9, 2025 Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci