An kammala bikin bayar da Kyautar Jaruman Indomie karo na 17, inda aka karrama matasan da suka nuna hazaƙa da jarumtaka, kuma suka zama jakadun Najeriya a fannoni daban-daban.

Wannan gagarumin biki ya gudana a birnin Legas a ranar 16 ga Oktoba, 2025, ƙarƙashin shirye-shiryen kamfanin Dufil Prima Foods, masu samar da Indomie Instant Noodles, a wani ɓangare na shirin kamfanin na kyautata dangantaka da al’umma (CSR).

Kamfanin ya tabbatar da bayar da kyaututtuka ga Jaruman Indomie — wani girmamawa na musamman ga matasan da suka nuna jarumta da Ƙirƙire-ƙirƙire a faɗin ƙasar.

Taken bikin na bana shi ne “Jaruman da Ba a San Su ba”, inda fitattun matasa uku daga sassan Najeriya suka fito a matsayin zakaru, bayan sun nuna bajinta, halin kirki, da jarumta.

Daga ranar 11 zuwa 13 ga Oktoba, 2025, miliyoyin ’yan Najeriya suka bibiyi shirye-shiryen talabijin na ƙasa domin jin labaran waɗannan matasa masu ban mamaki, waɗanda suka motsa zukata tare da ƙarfafa gwiwar al’umma.

Bayan wani dogon tsarin tantancewa da aka gudanar a duk faɗin ƙasar — wanda ya haɗa da hirarraki da makarantu da al’umma — an zaɓi zakaru uku daga rukuni daban-daban:

Abraham Umoren, mai shekaru 9 daga Jihar Akwa Ibom, ya lashe gasar Physical Bravery — jarumta ta zahiri.

Ismail Muhammad, mai shekaru 13 daga Jihar Kwara, ya lashe gasar Social Bravery — jarumta ta zamantakewa.

Hassan Adamu, mai shekaru 15 daga Jihar Yobe, ya lashe gasar Intellectual Bravery — jarumta ta basira.

An zaɓi waɗannan jarumai ne daga dubban matasa da aka gabatar daga sassa daban-daban na ƙasar, bayan watanni na bincike da tantancewa daga kwamitin masu zaman kansu da Dufil Prima Foods ta amince da su.

Da yake jawabi a ƙarshen bikin, Manajan Sadarwa na Rukunin Kamfanoni na Dufil Prima Foods, Temitope Ashiwaju, ya ce: “Kowace shekara muna ganin zurfin jarumta, fasaha, da baiwar da yaran Najeriya ke nunawa. Wannan shiri ne da muke alfahari da shi domin tallafa wa matasa wajen ciyar da ƙasa gaba.”

Ya ƙara da cewa: “Kyautar Jaruman Indomie ba kawai biki ba ne, amma madubi ne da ke nuna makomar Najeriya. Labaran waɗannan yara suna tunatar da mu cewa jarumta ba ta takaitu ga shekaru ko matsayi ba, sai dai a cikin ayyukan da ke ɗaga darajar wasu.”

Zakarun matasan sun nuna farin ciki da godiya bisa wannan dama, inda kowannensu ya gode wa Indomie saboda wannan girmamawa, tare da yin alƙawarin ci gaba da yin abin alheri a cikin al’ummominsu.

“Ba mu taɓa tsammanin za a yi irin wannan biki ba,” in ji Abraham Umoren, yana ƙara da cewa: “Na gode Indomie. Zan ci gaba da taimaka wa wasu gwargwadon iyawata.”

A bana, an gudanar da wannan biki na farko a matakin jihohi, inda aka girmama matasa daga kowanne rukuni, tare da faɗaɗa damar da aka samu don karrama ƙarin matasa masu kawo sauyi a Najeriya.

Tun daga lokacin da aka fara wannan shiri a shekarar 2008, matasa 59 suka riga sun amfana da tallafin karatu na miliyoyin naira — a matsayin yabo da ƙarfafa gwiwarsu don ci-gaban al’umma.

Bikin na bana ya bai wa iyalai, malamai, da shugabanni damar jin labaran da ke ci gaba da karfafa bege da juriya a cikin al’ummomi.

Kyautar Jaruman Indomie ta ci gaba da zama shaida ga jajircewar kamfanin Dufil Prima Foods, wanda ya daɗe yana ƙoƙarin haɓaka shugabanci, nuna tausayi, da kishin ƙasa a cikin manufofinsa na cigaban Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jarunta Kyautar Jaruman Indomie

এছাড়াও পড়ুন:

Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce

Zuwa karfe 5:41 na daren ranar 7 ga watan Disamba, fim din Amurka “Zootopia 2” wanda aka fara nuna wa kwanaki 12 da suka wuce (tun daga ranar 26 ga Nuwamba), ya samu kudaden shiga a cikin kasar Sin da yawansa ya wuce yuan biliyan 30 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 424.8, adadin da ya zarce kudaden shiga da ya samu a kasashen Arewacin Amurka, har ya sa kasar Sin ta zama kasa mafi taka rawa wajen samar da kudin shiga ga wannan fim a duniya. Hakan kuma ya nuna yadda Sin ke da babbar kasuwar fina-finai.

Ibrahim Akopari Ahmed, jami’in kula da harkokin cinikayya a Najeriya, a zantawarsa da dan jarida a baya, ya taba bayyana cewa, “Najeriya na daya daga cikin manyan kasashe mafiya karfin tattalin arziki a Afirka, kuma sana’o’i masu alaka da samar da hidimomi ne ke ba da gudunmawa mafi yawa ga GDPn kasar, wanda ya zarce kashi 50 cikin 100 na GDP. Saboda haka, Najeriya tana da karfi a bangaren sana’o’in samar da hidimomi, musamman a fagen nishadantarwa, kamar masana’antun samar da fina-finai ta Najeriya (Nollywood). A wannan fage, muna kan gaba a Afirka.”

Najeriya babbar kasa ce ta samar da fina-finai a Afirka, yayin da Sin ke da babbar kasuwar kallon fina-finai. Hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu ta fannin fina-finai yana da makoma mai haske, kuma a hakika Sin da Najeriya na karfafa hadin gwiwa a wannan fanni. Alal misali, an gudanar da bikin fina-finai na kasa da kasa na Zuma karo na 15 a farkon wannan watan a babban birnin Najeriya Abuja, inda aka nuna fina-finai biyu daga Sin: wato “Rooting” da “Shen Zhou 13”. Babban manajan kamfanin samar da fina-finai ta Najeriya Ali Nuhu ya bayyana cewa, yana fatan ta wannan taron, za a kara zurfafa hadin gwiwar sana’o’in samar da fina-finai tsakanin Sin da Najeriya. Muna fatan a karkashin tsarin “dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka” da ma sauran irin dandalin hadin gwiwa, Sin da Najeriya za su kara karfafa huldar al’adunsu, ta yadda a nan gaba za a samu karuwar shigowar kyawawan fina-finai daga Najeriya zuwa nan kasar Sin, don baiwa masu kallo na kasar Sin karin damammaki na fahimtar Afirka, musamman Najeriya.(Mai zane da rubutu: MINA)

ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Ya Kamata Amurka Ta Daina Sa Hannu Cikin Harkokin Najeriya December 4, 2025 Ra'ayi Riga Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi December 4, 2025 Ra'ayi Riga Layin Dogon Da Zai Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu November 29, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
  • Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin da miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • ’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba