Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Published: 29th, October 2025 GMT
Sanarwar ta ce, wannan horo mai taken ‘Computer Appreciation Training’ an shirya shi ne ta Hukumar Fasaha da Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), a matsayin babban taron ƙarawa juna sani ga manyan jami’an gwamnati.
A jawabinsa yayin buɗe shirin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa wannan horo wata muhimmiyar hanya ce wajen cimma burin gwamnatinsa na ingantaccen aiki ta amfani da fasaha.
Ya ce, “Burin mu shi ne tabbatar da cewa kowane bangare na gwamnati yana aiki cikin tsari, inganci da sauri, kamar yadda fasaha ke bai wa duniya damar gudanar da aiki cikin sauƙi.
“Mun shiga wani zamani ne da fasaha ke sauya yadda ake gudanar da mulki – daga tsarin tsara manufofi, yanke shawara, zuwa yadda ake sadarwa da isar da ayyuka ga jama’a. A yau, sanin amfani da kwamfuta ba zaɓi ba ne, wajibi ne ga duk wanda ke aikin gwamnati.”
Gwamna Lawal ya ce, hukumar ZITDA ta ƙaddamar da muhimman shirye-shirye kamar Zamfara e-Governance Platform (e-GovConnect), tsarin Digital Literacy Framework, da kuma haɗin gwiwa da manyan kamfanonin fasaha na duniya don ƙarfafa ilimin fasaha a jihar.
Ya kuma buƙaci mahalarta da su ɗauki shirin da muhimmanci, yana mai cewa ilimin da za su samu a wajen zai taimaka wajen ƙara inganta aiki, gaskiya da ingantaccen hidima ga jama’a.
“Mutanenmu sun cancanci gwamnati mai wayewa kuma mai amsawa cikin gaggawa ga buƙatunsu. Wannan canjin kuwa, ‘yan uwa, yana farawa da mu. Bayan wannan shirin, za a gudanar da jarrabawa domin tantance abin da aka koya, wanda kuma zai zama wani bangare na kimanta aikin kowane jami’i,” in ji gwamnan.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu
An ɗage sauraron shari’ar tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, matarsa Hafsat, da wasu mutum shida a ranar Litinin bayan sun kasa miƙa takardun da ake buƙata a kotu.
Gwamnatin Jihar Kano ta gurfanar da su bisa tuhume-tuhume 11 da suka shafi cin hanci, haɗa baki wajen yin laifi, da karkatar da kuɗaɗen gwamnati da suka kai miliyoyin Naira.
APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar SayawaLokacin da aka fara sauraren shari’ar, lauya mai kare gwamnati, Adeola Adedipe (SAN), ya ce sun shirya fara gabatar da shaidu, amma lauyoyin Ganduje da sauran waɗanda ake tuhuma suka nemi ƙarin lokaci, inda suka bayyana cewar ba a ba su wasu takardu ba.
Alƙalin kotun, Mai Shari’a Amina Adamu-Aliyu, ta umarci dukkanin ɓangarorin su kammala miƙa takardunsu kafin zaman kotun na gaba, sannan ta ɗage shari’ar zuwa 26 ga Nuwamba, 2025.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA