Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Published: 29th, October 2025 GMT
Sanarwar ta ce, wannan horo mai taken ‘Computer Appreciation Training’ an shirya shi ne ta Hukumar Fasaha da Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), a matsayin babban taron ƙarawa juna sani ga manyan jami’an gwamnati.
A jawabinsa yayin buɗe shirin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa wannan horo wata muhimmiyar hanya ce wajen cimma burin gwamnatinsa na ingantaccen aiki ta amfani da fasaha.
Ya ce, “Burin mu shi ne tabbatar da cewa kowane bangare na gwamnati yana aiki cikin tsari, inganci da sauri, kamar yadda fasaha ke bai wa duniya damar gudanar da aiki cikin sauƙi.
“Mun shiga wani zamani ne da fasaha ke sauya yadda ake gudanar da mulki – daga tsarin tsara manufofi, yanke shawara, zuwa yadda ake sadarwa da isar da ayyuka ga jama’a. A yau, sanin amfani da kwamfuta ba zaɓi ba ne, wajibi ne ga duk wanda ke aikin gwamnati.”
Gwamna Lawal ya ce, hukumar ZITDA ta ƙaddamar da muhimman shirye-shirye kamar Zamfara e-Governance Platform (e-GovConnect), tsarin Digital Literacy Framework, da kuma haɗin gwiwa da manyan kamfanonin fasaha na duniya don ƙarfafa ilimin fasaha a jihar.
Ya kuma buƙaci mahalarta da su ɗauki shirin da muhimmanci, yana mai cewa ilimin da za su samu a wajen zai taimaka wajen ƙara inganta aiki, gaskiya da ingantaccen hidima ga jama’a.
“Mutanenmu sun cancanci gwamnati mai wayewa kuma mai amsawa cikin gaggawa ga buƙatunsu. Wannan canjin kuwa, ‘yan uwa, yana farawa da mu. Bayan wannan shirin, za a gudanar da jarrabawa domin tantance abin da aka koya, wanda kuma zai zama wani bangare na kimanta aikin kowane jami’i,” in ji gwamnan.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ƙaryata zargin cewa Gwamna Bala Mohammed na shirin ficewa daga PDP zuwa jami’yyar PRP.
Jita-jitar ta samo asali ne bayan Sakataren jam’iyyar PRP na Bauchi, Hon. Wada Abdullahi, ya ce ba za su karɓi gwamnan zuwa jami’yyarsu ba.
Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-ZakzakyYa ce gwamnan bai cika ƙa’idojin da PRP ke buƙata ba a shugabancinsa a Bauchi.
Amma mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin yaɗa labarai, Mukhtar Gidado, ya ce gwamnan bai taɓa tunanin barin PDP ba.
Ya ce babu wata tattaunawa ko mataki da aka ɗauka na komawa PRP.
Gidado, ya ce gwamnan na aiki ne wajen ƙarfafa PDP kuma ya taɓa doke PRP a zaɓuka da suka gabata.
Ya ƙara da cewa Jihar Bauchi ta samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnan, musamman a ɓangaren tallafa wa jama’a, ababen more rayuwa, ci gaban ƙauyuka, da yawon buɗe ido.
Gwamnatin ta soki PRP kan yaɗa jita-jita marasa tushe.
Ya ce gwamnan na da ’yancin zaɓar makomarsa a harkokin siyasa, amma duk wata shawara da zai ɗauka ba za ta kasance bisa ƙarya ko jita-jita ba.