Gwamnatin kasar Kamaru ta ce za ta dauki matakin shari’a kan babban jagoran adawar kasar, Issa Tchiroma Bakary, bisa zarginsa da tayar da tarzoma bayan zaben shugaban ƙasa.

Ministan cikin gida na kasar, Paul Atanga Nji, ne ya bayyana hakan a ranar Talata, kamar yadda rahotannin kafafen yaɗa labarai suka nuna.

Ba daidai ba ne Tinubu ya ci gaba da ciyo bashi duk da cire tallafin mai – Sanusi DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyya

Ya ce hukumomin kasar sun fara tattara saƙonnin kafafen sada zumunta da bidiyo da aka bayyana a matsayin “ƙarya” da kuma masu tayar da hankali domin a gurfanar da masu wallafa su a gaban kotu, “kamar yadda ɗan takara Issa Tchiroma da abokan aikinsa ke da alhakin shirin tayar da tarzoma da nufin jefa ƙasar cikin rudani,” in ji Nji a taron manema labarai da aka gudanar a Yaoundé, babban birnin kasar.

Sakamakon zaben da Majalisar Dokoki ta ƙasa ta bayyana a ranar Litinin ya nuna cewa Shugaba Paul Biya ya sake lashe shi da kaso 53.66 cikin 100 na ƙuri’u, inda ya samu wa’adin mulki na takwas.

Hakan dai na nufin zai ci gaba da shugabanci na shekaru 43, kuma zai kasance matsayin shugaban ƙasa mafi dadewa a kan karagar mulki a duniya.

Issa Tchiroma ya bayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaben da aka gudanar a ranar 12 ga Oktoba.

Magoya bayansa, da suka amsa kiran yin zanga-zanga a ranar Lahadi, sun yi taho-mu-gama da jami’an tsaro kafin sanar da sakamakon, lamarin da ya haifar da mutuwar akalla fararen hula hudu.

Nji ya ce duk da wasu ƙananan rikice-rikice da aka samu, an samu daidaito a fannin tsaro, yana mai cewa an kammala dukkan tsarin zabe bayan sanarwar sakamakon da Majalisar Dokoki ta fitar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Issa Tchiroma Bakary Kamaru Paul Biya

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto jaririya ’yar mako daya da haihuwa da aka sayar a Anambra

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Anambra ta ce ta ceto wata jaririya da ba ta wuce mako daya da haihuwa ba, da aka sayar kan kuɗi Naira miliyan ɗaya da rabi, tare da cafke mata huɗu da ake zargin su da hannu a cinikin.

Kakakin rundunar a jihar, SP Tochukwu Ikenga, ya shaida wa Aminiya cewa an samu labarin sayar da jaririyar ne a kauyen Ifite-Awkuzu da ke Karamar Hukumar Oti, inda rundunar ta ɗauki matakin gaggawa na cafke waɗanda ake zargin.

An kai ƙarar malamai 2 kan zargin ɓatanci ga Annabi a Kaduna Uwa da ’yarta sun nitse a hatsarin jirgin ruwa a Borno

Waɗanda aka kama sun haɗa da Elizabeth Okafor mai kimanin shekara 62, Esther Nweke mai shekara 48, Ngozi Maanfa mai shekara 45, da Peace Elijah Moses, wadda ita ce mafi ƙarancin shekaru a cikin su, mai kimanin shekara 25.

Ikenga ya ce binciken da rundunar ta gudanar ya tabbatar da cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin sayen jaririyar ba tare da an tursasa su ba, kuma ba a yi masu duka ko azabtarwa ba kafin su bayyana gaskiya.

“Jaririyar tana cikin ƙoshin lafiya, ba ta samu wata matsala ba,” in ji Ikenga.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ikioye Orutugu, ya bayar da umarnin a mika waɗanda ake zargin zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) domin ci gaba da bincike.

Ya ce bayan kammala binciken, za a gurfanar da su a gaban kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ceto jaririya ’yar mako daya da haihuwa da aka sayar a Anambra
  • JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
  • Majalisar Dattawa za ta tantance sabbin hafsoshin tsaro ranar Laraba
  • Rikicin adawa da cin zaben Shugaba Paul Biya ya bazu a Kamaru
  • Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
  • Kamaru : Paul Biya, ya lashe zaben shugaban kasa a karo na takwas
  • Paul Biya mai shekara 92 ya lashe zaɓen Kamaru
  • Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa
  • Ana Zaman dar-dar a Kamaru gabanin bayyana sakamakon zaben shugaban kasa