Aminiya:
2025-10-30@23:15:03 GMT

Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket

Published: 30th, October 2025 GMT

Wani haziƙin matashin ɗan wasan Cricket mai shekara 17 ɗan asalin ƙasar Australiya ya mutu a yau Alhamis bayan ƙwallo ta buge shi a lokacin wasa.

Ƙwallon ta bugi, Ben Austin a wuyansa ne duk da cewa yana sanye da hular kariyar kai (Helmet) a lokacin da yake ƙoƙarin kare ƙwallon da aka bugo.

Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja

Nan take aka garzaya da shi asibiti cikin mawuyacin hali, daga bisani rai ya yi halinsa.

“Mun yi matuƙar baƙin ciki da rasuwar haziƙi Ben ɗinmu, wanda ya mutu da safiyar yau Alhamis,” in ji mahaifinsa Jace Austin a cikin wata sanarwa.

A cewar jaridar ABC News, matashin ɗan wasan bai sanya rigar da ke kare wuyansa ba, hakan ne ya sa ƙwallon ta dufafe shi.

Austin ya kasance ƙwararren mai buga ƙwallo, wanda ƙungiyarsa ta Ferntree Gully Cricket Club ta ɗauke shi a matsayin “ɗan wasan Cricket mai hazaka, babban jagora kuma matashi mai ban mamaki”.

‘Yan wasa daga ƙungiyoyin biyu na India da Australia a ɓangaren mata da ke buga wasan Cricket na duniya sun sanya baƙaƙen kambu domin alhinin mutuwarsa.

Yau dai kimanin shekaru 11 rabon da wani ɗan wasan Cricket ya mutu a lokacin wasa, tun bayan da shahararren ɗan wasan nan ɗan asalin ƙasar Australia Test Phillip Hughes ya mutu a 2014.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ɗan wasan Cricket

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Shugaba Bola Tinubu ya yi wa sabbin Shugabannin Sojoji ado da karin girma domin su dace da sabbin muƙamansu. Sabbin shugabannin rundunar sojin kasar da aka yi wa ado sun hada da Laftanar Janar, wanda yanzu ya zama Janar Olufemi Olatubosun Oluyede, a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS); da kuma Manjo Janar yanzu ya koma Laftanar Janar Emmanuel Undiendeye Undiendeye a matsayin Babban Hafsan Tsaro na farin kaya (CDI). Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  Sauran su ne Manjo Janar, wanda yanzu ya zama Laftanar Janar Waidi Shaibu a matsayin Babban Hafsan Soja (COAS); Air Vice Marshal, wanda yanzu ya zama Air Marshal Kevin Aneke a matsayin Babban Hafsan Sojan Sama; da kuma Rear Admiral, wanda yanzu ya zama Vice Admiral Idi Abbas a matsayin Babban Hafsan Sojan Ruwa. Shugaba Tinubu ya sanar da maye gurbin Shugabannin Rundunar tsaron ne a ranar Juma’ar da ta gabata, wani mataki da aka danganta da bukatar sake mai da hankali da kuma karfafa tsaron kasa. Bayan haka, Shugaba Tinubu ya bukaci sabbin Shugabannin Rundunar tsaron da su dauki mataki mai tsauri kan barazanar tsaro da ke tasowa a fadin kasar, yana mai gargadin cewa ‘yan Nijeriya na tsammanin ganin sakamako, ba uzuri ba. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray
  • Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
  • Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti
  • Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba
  • Matashi ya rasa ransa a kan soyayya a Yobe
  • Senegal ta sake gano wasu shaidu kan kisan  gillar da aka yi a lokacin mulkin mallaka
  • An raba wa iyalan ’yan sandan da suka mutu tallafin N31m a Jigawa
  • Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi