An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing
Published: 26th, October 2025 GMT
Yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke shirin tafiya kasar Koriya ta Kudu, domin halartar kwarya-kwaryar taron shugabanni karo na 32, na kungiyar hadin-gwiwar tattalin arzikin kasashen yankin Asiya da Pasifik wato APEC, tare da gudanar da ziyarar aiki a kasar, an gudanar da wani taron tattaunawa, mai taken “Shugabancin duniya da samun wadata tare a yankin Asiya da Pasifik” a nan birnin Beijing, wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG, da jami’ar Yonsei da gidan talabijin na YTN na Koriya ta Kudu suka shirya tare.
Yayin taron, shugaban CMG Shen Haixiong, ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo, inda ya ce “CMG na fatan yin hadin gwiwa mai zurfi tare da kasashen yankin Asiya da Pasifik, don haka ya dace mu ba da labaran hadin gwiwa tare, mu kirkira, kuma mu bunkasa musayar al’adu, mu shiga tattaunawa da hadin gwiwa, sannan mu ba da gudummawar hikimomi da karfinmu, wajen kyautata tsarin shugabancin duniya”. (Safiyah Ma)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Asiya da Pasifik Asiya Da Pasifik
এছাড়াও পড়ুন:
Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
Daga Isma’il Adamu
Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa tana da kwarin gwiwar lashe karin mukaman siyasa a zaben shekarar 2027, ciki har da na shugaba kasa da gwamnan Jihar Katsina.
Sabon shugaban jam’iyyar da aka rantsar a Jihar Katsina, Alhaji Armaya’u AbdulKadir ne ya bayyana haka a zaben shugabannin jam’iyyar da aka gudanar a Katsina.
Ya ce jam’iyyar, wacce ta ba da muhimmanci ga ilimi, walwalar jama’a, karfafa matasa da ci gaban abubuwan more rayuwa, ta kara samun farin jini a wajen jama’a saboda ingantaccen jagoranci da wakilcin da take bayarwa ta hannun mambobinta da ke rike da mukamai a matakin kananan hukumomi, jihohi da tarayya.
“Masu zabe sun ga abin da jam’iyyarmu ke aiwatarwa. ‘Yan majalisa da sauran wadanda aka zaba suna aiki a matakai daban-daban tun daga kananan hukumomi har zuwa matakin tarayya. ‘Yan Najeriya sun shaida kwarjininmu, shi ya sa muke da tabbacin lashe karin kujeru a zaben 2027.
“Jagoranmu na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya kuduri aniyar karbar shugabancin kasa, yayin da a nan Jihar Katsina kuma muke shirin tsayar da kwararru masu kwarewa da kuzari da za su iya lashe kujerar Gwamna da sauran mukaman zabe.”
AbdulKadir, wanda ya jaddada cewa NNPP na kara samun karbuwa a tsakanin ‘yan Najeriya, ya ce hakan ya nuna a kwanan nan ta hanyar sauya sheka da wasu ‘yan wasu jam’iyyu suka yi zuwa NNPP. Ya kuma bukaci mambobin jam’iyyar da su kara samun magoya baya domin tunkarar zaben 2027.
Zaben shugabannin jihar, wanda ya samar da mambobi 38 ta hanyar maslaha, ya samu kulawar INEC da hukumomin tsaro, tare da halartar wakilan jam’iyyar daga kasa da yankin Arewa maso Yamma, da kuma daruruwan mambobin jam’iyyar.
Alhaji Armaya’u AbdulKadir ya kasance Shugaban jam’iyya, Sani Arga mataimaki na farko, Tijjani Zakari sakatare, Umar Musa sakataren shirya ayyuka, sannan Hauwa Abubakar ta zama shugabar mata.
Tunda farko, shugaban kwamitin gudanar da taron, Alhaji Muhammad Yusuf-Fagge, ya yaba wa wakilai da mambobin jam’iyyar a jihar bisa ladabi da natsuwar da suka nuna a yayin taron, da kuma yadda suka amince da hanyar maslaha wacce “ta sauƙaƙa aikin.”
Ya yi kira ga mambobin jam’iyyar a jihar da su ci gaba da kasancewa cikin hadin kai, biyayya da ladabi, tare da kara yawaita mambobi da samun goyon baya ga jam’iyyar a jihar.