Aminiya:
2025-10-30@17:53:30 GMT

Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja

Published: 30th, October 2025 GMT

Rahotanni sun bayyana cewa, wata gobara ta ƙone wani shagon Adidas Sports da ke cikin rukunin babban kantin nan na sayar da kayayyaki na Jabi Lake Mall, Abuja da tsakar daren Alhamis.

Daily Trust ta ruwaito cewa, shagon ne kaɗai gobarar ta shafa.

An kuma samu rahoton cewa, an baza jami’an kashe gobara daga Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, da na Kamfanin Berger da na hukumar kashe gobara ta Abuja da kuma jami’an ’yan sanda zuwa wurin.

Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29

A lokacin da Wakilin Daily Trust ya kai ziyara da safe zuwa wurin, an shawo kan gobarar.

Wani ma’aikaci a shagon ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na tsakar daren ranar Alhamis.

Ya ce, ba a samu asarar rai ba a wurin. Ya kuma tabbatar da cewa, “Shagon sayar da kayan Wasannin Adidas ne kawai gobarar ta shafa.”

Mai magana da yawun Hukumar kashe gobara ta babban birnin tarayya, Ibrahim Mohammad, ya tabbatarwa da majiyar da faruwar lamarin, amma ya ce ƙarama ce.

Ya ce, an shawo kan lamarin kuma an dawo da zaman lafiya.

Ita ma da take mayar da martani, kakakin rundunar ’yan sandan Birnin Tarayya, Josephine Adeh ta ce an tura jami’an ’yan sanda wurin da lamarin ya faru domin kare yankin da kuma hana sace-sacen jama’a.

“Mun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3:40 na asubahi, nan take muka tura mutanenmu wurin domin su tsare wurin da kuma hana duk wani abu da ya saɓa wa zaman lafiya,” in ji ta.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa za ta tantance sabbin hafsoshin tsaro ranar Laraba

Majalisar Dattawa za ta gudanar da zaman tantance manyan hafsoshin tsaron ƙasar a gobe Laraba waɗanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa kwanan nan.

Shugaba Tinubu ya aike da sunayen sabbin hafsoshin zuwa majalisar ne domin tantancewa da amincewa da su, kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada.

Rikicin adawa da cin zaben Shugaba Paul Biya ya bazu a Kamaru ’Yan bindiga sun sa harajin N15m kan al’ummar Mazabar Sanata Tambuwal

A wata wasiƙar fadar shugaban ƙasa da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya karanta yayin zaman da aka gudanar a wannan Talatar, ya ce kwamitin da ke kula da harkokin tsaro zai zauna gobe domin tantance waɗanda aka naɗa.

A makon jiya ne Shugaba Tinubu ya aiwatar da sauye-sauye a bangaren tsaro, inda ya ɗaga likafar Laftanar Janar Oluyede Olupemi daga babban hafsan sojin ƙasa zuwa babban hafsan tsaron ƙasa, don maye gurbin Janar Christopher Musa da aka cire daga muƙaminsa.

Haka kuma, shugaban ƙasar ya naɗa sababbin hafsoshin sojin sama, ruwa da ƙasa, yayin da ya bar Manjo Janar E.A.P. Undiendeye a matsayinsa na babban hafsan sashen tattara bayanan sirri na sojin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta bai wa ASUU N2.3bn domin biyan bashin albashin malamai
  • Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC
  • Jami’ar MDD Ta Musamman A Falasdinu Ta Soki Shirin Trump Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Larijani: Dangantakar Iran da Pakistan na iya komawa babban hadin gwiwa a tsakaninsu
  • Majalisar Dattawa za ta tantance sabbin hafsoshin tsaro ranar Laraba
  • Jami’an tsaro sun harbi matar aure sun lakaɗa wa jama’a duka a Katsina 
  • ’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
  • Jami’an tsaro sun kashe ’yan bindiga 80 a Kebbi
  • An kashe wasu makiyaya 10 a Kebbi