Aminiya:
2025-12-15@04:38:16 GMT

Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja

Published: 30th, October 2025 GMT

Rahotanni sun bayyana cewa, wata gobara ta ƙone wani shagon Adidas Sports da ke cikin rukunin babban kantin nan na sayar da kayayyaki na Jabi Lake Mall, Abuja da tsakar daren Alhamis.

Daily Trust ta ruwaito cewa, shagon ne kaɗai gobarar ta shafa.

An kuma samu rahoton cewa, an baza jami’an kashe gobara daga Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, da na Kamfanin Berger da na hukumar kashe gobara ta Abuja da kuma jami’an ’yan sanda zuwa wurin.

Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29

A lokacin da Wakilin Daily Trust ya kai ziyara da safe zuwa wurin, an shawo kan gobarar.

Wani ma’aikaci a shagon ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na tsakar daren ranar Alhamis.

Ya ce, ba a samu asarar rai ba a wurin. Ya kuma tabbatar da cewa, “Shagon sayar da kayan Wasannin Adidas ne kawai gobarar ta shafa.”

Mai magana da yawun Hukumar kashe gobara ta babban birnin tarayya, Ibrahim Mohammad, ya tabbatarwa da majiyar da faruwar lamarin, amma ya ce ƙarama ce.

Ya ce, an shawo kan lamarin kuma an dawo da zaman lafiya.

Ita ma da take mayar da martani, kakakin rundunar ’yan sandan Birnin Tarayya, Josephine Adeh ta ce an tura jami’an ’yan sanda wurin da lamarin ya faru domin kare yankin da kuma hana sace-sacen jama’a.

“Mun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3:40 na asubahi, nan take muka tura mutanenmu wurin domin su tsare wurin da kuma hana duk wani abu da ya saɓa wa zaman lafiya,” in ji ta.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja

Shugabannin kasashen kungiyar Tattalin Arzikin kasashen Yammacin Afirka ECOWAS sun hallara a birnin Abuja na  Najeriya don bude babban taron koli da za’a fara yau Lahadi.

Bayanai sun ce rashin tsaro da kuma Juye-juyen Mulki musamman masu sarkakiya da aka samu a Guinea Bissau da kuma yunkurinsa a jamhuriyar Benin shi ne ake ganin taron  zai fi mayar da hankali a yayin wannnan taron  na musamman.

Taron na zuwa ne mako daya bayan yunkurin kifar da gwamnatin Benin da Shugaban kasar Patrice Talon ke jagoranta a kwatano, da kuma damuwa kan rikicin siyasa a Guinea-Bissau da tabarbarewar tsaro a arewacin kasashen gabar tekun yammacin Afirka.

Wannan shi ne taron koli na farko da Shugaban kasar Sierra Leone Julius Maada Bio ke jagoranta a matsayinsa na shugaban kungiyar ECOWAS, inda ake sa ran zai jagoranci yanke muhimman shawarwari kan tsaron yankin.

Ana sa ran taron na Abuja zai kuma zama dandalin kammala bikin cika shekaru 50 da kafuwar ECOWAS, tare da yanke shawarwari kan matakan da kungiyar za ta dauka domin tunkarar kalubalen tsaro da siyasa da ke kara Ta’azzara a yankin yammacin Afirka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha December 14, 2025 Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan. December 14, 2025 Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai December 14, 2025 Ghana Ta Kori Wasu Yahudawa Guda 3 Don Mayar Da Martani December 14, 2025 Araghchi ya bukaci Amurka ta girmama al’ummar Iran da gwamnatinta December 14, 2025 Dan bindiga ya kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula a Siriya December 14, 2025 Mutum biyu sun mutu a harbin bindiga a Jami’ar Brown ta Amurka December 14, 2025 Shugabannin kasashen (ECOWAS) na taro a Abuja December 14, 2025 Kasashen AES zasu kafa bankin dogaro da kai December 14, 2025 Sheikh Na’im Kassim: Idan Duniya Baki Daya Za Ta Taru, Ba Wanda Zai Iya Kwace Makaman Hizbullah December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano
  • َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja
  • Farfesa Gumel Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Da Ke Dutse
  • Shugabannin kasashen (ECOWAS) na taro a Abuja
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano