Aminiya:
2025-12-15@06:56:51 GMT

Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum

Published: 30th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Umara Zulum ya sanar da fara fitar da kayayyakin robobi zuwa ƙasashen duniya wanda hakan ke nuna wani gagarumin ci gaba a wani ɓangare na ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arzikin Jihar.

Gwamnan ya jaddada cewa, wannan matakin wani ɓangare ne na babbar ajanda na bunƙasa masana’antu da kuma kawar da dogaro da jihar kan yi na kason da gwamnatin tarayya ke bayarwa duk wata.

Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti

Zulum ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis yayin rangadin duba masana’antar robobi ta Borno da ke cikin yankin masana’antu na Maiduguri.

“Ina farin cikin lura cewa mutanen Jihar Borno ba za su sake sayen kayan robobi daga wasu wurare ba, kun ga an sayar da kayayyakin ga ƙasashen maƙwabta da sauran jihohi a cikin Najeriya.”

“Za mu zuba jari sosai a masana’antunmu, don haka nan gaba kaɗan, gwamnatin Jihar Borno ba za ta sake dogara da asusun tarayya ba don ayyukanta na yau da kullum,” in ji Zulum.

Gwamnan ya bayyana cewa masana’antar ta fara fitar da kayayyakinta ga ƙasashen waje, tare da jigilar kayayyakin filastik da aka gama zuwa ƙasashe maƙwabta kamar Chadi da Jamhuriyar Kamaru.

Zulum ya lura cewa an fara gina cibiyar ne a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Kashim Shettima, amma an farfaɗo da ita a matsayin wani ɓangare na shirin murmurewa da ci gaban gwamnatinsa.

Wasu daga cikin kayan robobin

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnan Jihar Borno Umara Zulum

এছাড়াও পড়ুন:

ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka

Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), ta yi alƙawarin kare dimokuraɗiyya da kuma inganta tsaro a yankin Yammacin Afirka.

Wannan alƙawarin na zuwa ne a dai-dai lokacin da yankin ke fuskantar matsalolin tsaro da na juyin mulki.

Yadda aka yi bikin naɗa Rarara sarkin wakar ƙasar Hausa a Daura Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano

An yanke wannan shawara ne a taron shugabannin ƙasashen ECOWAS karo na 68, wanda aka gudanar a Abuja a ranar Lahadi.

Shugaba Bola Tinubu, wanda Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya wakilta, ya yi kira ga ƙasashen ECOWAS da su zauna lafiya tare da haɗa kai.

Ya yi gargaɗi ncewa ƙungiyar tana samun rauni idan ƙasashe suka rabu.

Ya ce ƙasashen Yammacin Afirka ba wai waje ɗaya suka haɗa ba, face suna da tarihi, al’adu da gwagwarmaya iri ɗaya da ta haɗa su.

Shugaba Tinubu, ya bayyana cewa duk da cewa rashin jituwa na iya faruwa tsakanin ƙasashe, bai kamata hakan ya karya zumunci da makomar ƙasashen yankin ba.

Ya zayyano matsalolin da yankin ke fuskanta, kamar ta’addanci, rikice-rikice, tsattsauran ra’ayi, juyin mulki, laifukan ƙetare iyaka, yawaitar makamai, barazana a Intanet, sauyin yanayi, ƙarancin abinci da sauransu.

Ya ce waɗannan matsaloli ba su da iyaka, kuma ƙasa ɗaya ba za ta iya magance su ba.

Tinubu ya tarbi shugabannin ECOWAS zuwa Abuja, inda ya yi fatan taron zai ƙara amincewa da juna, ƙarfafa haɗin kai, tare da sake ɗora ECOWAS bisa ginshiƙan adalci da makoma ɗaya.

A yayin taron, ECOWAS ta kuma mayar da hankali kan bunƙasar tattalin arziƙi ta hanyar kamfanoni masu zaman kansu.

Shugaban Hukumar ECOWAS, Dokta Omar Alieu Touray, ya sanar da kafa Majalisar Kasuwanci ta ECOWAS.

An naɗa fitaccen ɗan kasuwan Najeriya, Alhaji Aliko Dangote, a matsayin shugaban farko na wannan majalisa.

Shugaban ƙasar Saliyo kuma Shugaban ECOWAS, Julius Maada Bio, ya bayyana taron a matsayin mai muhimmanci.

Ya ce yankin Yammacin Afirka na fuskantar manyan ƙalubale na tsaro, dimokuraɗiyya da tattalin arziƙi, kuma shawarwarin da za a yanke za su shafi sama da mutum miliyan 400.

Ya kuma bayyana cewa an yi murnar cikar ECOWAS shekaru 50 da kafuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka
  • Hukumar Film ta kasa ta horar da marubuta 53 rubutun fim
  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • NEPC Ta Horas da Mata Kan Damar Kasuwancin Fitar da Kayayyaki Zuwa Kasashen Waje
  • An Fara Gyaran Tashar Talabijin Ta Jigawa Don Kara Mata Nisan Zango
  • DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa