Aminiya:
2025-10-27@11:36:55 GMT

Masu yabon Buhari sun yi masa ba’a bayan ya sauka daga mulki —Gwamna Sule

Published: 27th, October 2025 GMT

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce wasu daga cikin mutanen da saba yabon tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari lokacin yake kan mulki, su ne suka fara yi masa ba’a tare da suka bayan ya sauka daga mulki.

Da yake jawabi a wani taron “Lakcar Raymond Dokpesi” da Ƙungiyar Masana Hulɗa da Jama’a ta Najeriya (NIPR) ta shirya a birnin Abuja, Gwamna Sule ya ce ya shaida da idonsa yadda wasu ’yan siyasa ke yabo da fadanci a gaban Buhari, amma daga bisani su sauya baki sheƙa da zarar shugabannin sun bar mulki.

Ya ce, “Tun da na zama gwamna, na ga abin da son kai da kwaɗayi ke iya haifarwa. Na ga mutane suna zaune a gaban Shugaba Buhari suna cewa, ‘Kai ka fi kowa, babu wanda zai iya yin wannan kamar kai.’

“Amma bayan saukar Buhari daga mulki, sai suka fara cewa, ‘Ai, yana cikin shugabannin mafiya rauni.’ Waɗannan mutanen ɗaya ne, amma lokaci ne ya bambanta. Wannan shi ne kwaɗayin yabo da son kai,” in ji shi.

Mai mata ɗaya abin tausayi ne — Sanata Nwoko Saukar Farashin abinci: Manoma da gwamnati na nuna wa juna yatsa

A wajen taron, an karrama Gwamna Sule da kyauta da kuma lambar girmamawa ta NIPR, inda ya bayyana farin cikinsa da irin jarumtakar marigayi Cif Raymond Dokpesi, wanda ya kafa tashoshin rediyo da talabijin na farko masu zaman kansu a ƙasar tun lokacin mulkin soja.

“Ina nan ne don mu taya murna da tunawa da gwarzon kafafen yaɗa labarai. Dokpesi mutum ne mai gaskiya da jajircewa wajen faɗin gaskiya ga masu mulki, ko da a lokutan da suka fi wuya,” in ji Gwamna Sule.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari yabo Gwamna Sule

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Columbia Ya Yi Watsi Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Masa

Shugaba Gustavo Petro ya ce, ba wai kawai ba ya wata mu’amala ta kasuwanci da Amurka ba ne, ba shi ma da koda dala kwaya daya a cikin wani asusu na bankunan Amurkan balle a ce an rufe shi.

Gustavo ya kara da cewa; ko kadan ba zai taba rusunawa a gaban Amurka ba, ba kuma zai ja da baya ba.

A jiya Juma’a da marece ne dai Baitulmalin Amurka ya sanar da kakaba wa shugaban kasar ta Columbia takunkumi.

Gustavo ya kuma ci gaba da cewa; Yadda yake fada da yaduwar muggan kwayoyi na shekaru masu tsawo, shi ne ya sa Amurkan ta dauki wannan irin matakin akansa alhali kasarsa Columbia tana taimakawa wajen hana Amurkawan shan hodar Iblis.

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya taba zargin takwaransa na Columbia da cewa yana taimakawa wajen yaduwar hodar Iblis, tare da siffata shi a matsayin dillalin muggan kwayoyi.

 Amurka dai ta shiga tsama da Shugaban Columbia ne saboda siyasarsa ta kin jinin HKI da take tafka laifukan yaki a Gaza, bayan da kasarsa ta yanke duk wata alakar diplomasiyya da kasuwanci da ita.

A yayin taron babban zauren MDD a birnin New York, shugaban kasar ta Columbia ya yi kira da a kafa rundunar kasa da kasa domin kare al’ummar Falasdinu da HKI take yi wa kisan kiyashi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Kwallon Kafa Ta Futsal Ta Matan Iran Sun Sami Nasara Akan Kasar Bahrain October 25, 2025 Antonio Gutrress: MDD Tana Bukatuwa Da A Yi Ma Ta Kwaskwarima October 25, 2025 Lebanon: An Sami Shahidai 3 Sanadiyyar Hare-haren HKI A Kudancin Lebanon October 25, 2025 Iran Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Isra’ila Kan Kasar Lebanon October 24, 2025 Rasha Ta Jaddada Cewa: Kasashen Turai Sun Taka Doka Kan Batun Makamashin Nukiliyar Iran October 24, 2025 Ayatullahi Khatami Ya Ce: Shugaban Kasar Amurka Trump Dan Ta’adda Ne                                                                                October 24, 2025 Shugaban Amurka Ya Ce: Za Su Dauki Matakin Soji Kan Kasar Venezuela Nan Gaba Kadan October 24, 2025 Gwamnatin Iraki Ta Yi Allah Wadai Da Mamaye Yankin Yammacin Kogin Jordan Na Falasdinu October 24, 2025 ‘Yan Sandan Kasar Ghana Sun Tseratar Da ‘Yan Najeriya 57 Da Aka Yi Fasakwaurinsu October 24, 2025  Trump Ya Dakatar Da Tattaunawar Kasuwanci Da Kasar Canada October 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙaddamar da Kyautar Jaruman Indomie Karo Na 17 Yayin Da Zakarun Matasa Suka fafata daga karshe an samu zakaru
  • Sule Lamiɗo na neman takarar Shugaban PDP na Ƙasa
  • Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
  • Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa
  • ’Yan sanda sun taimaka wa ’yan daba rusa gidaje — Al’ummar Shendam
  • Shugaban Kasar Columbia Ya Yi Watsi Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Masa
  • Ƙungiya ta tallafa wa ɗaliban makarantar masu buƙata ta musamman a Gombe
  • ’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa
  • Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu