Gwamnatin Kaduna Tare Da AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma
Published: 26th, October 2025 GMT
Ya ƙara da cewa Kaduna ita ce jihar da ta cika ƙa’idojin da aka shimfiɗa a yarjejeniyar Malabo kan saka hannun jari a harkar noma.
Shugaban AUDA–NEPAD a Nijeriya, Honarabul Jabir Abdullahi Tsauni, ya yaba wa gwamnatin Jihar Kaduna bisa samar da kuɗaɗen haɗin gwiwa da suka bai wa shirin damar faɗaɗa zuwa dukkan ƙananan hukumomi 23 na jihar.
A cewar Tsauni, an horar da ƙanana manoma 345 kan kyawawan hanyoyin noma da kuma dabarun noma masu jituwa da yanayin sauyin yanayi, ciki har da noman lambu na gida irin su tumatir, barkono mai zaƙi, masara, wake, da waken soya.
Komashinan noma na Jihar Kaduna, Murtala Dabo, ya bayyana cewa wannan shiri ya nuna yadda Kaduna ke da niyyar mayar da noma a matsayin sana’ar da ke kawo riba, ba kawai hanyar rayuwa ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
’Yan bindiga sun kai sabon hari wasu yankuna na Jihar Sakkwato, inda suka kashe mutane huɗu tare da yin awon gaba da mata huɗu.
Wani mazaunin Gatawa, ya shaida wa Aminiya ce harin ya faru ne a daren ranar Asabar, lokacin da ’yan bindiga sama da goma suka shiga garin a kan babura.
Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar BeninA cewarsa, “Sun ratsa gefen gari suka dinga shiga gida-gida. Sun harbe mutane huɗu; uku sun mutu nan take, na huɗu kuma ya rasu a asibiti.”
Ya ƙara da cewa bayan harin, sojoji sun isa garin wanda hakan ya sa maharan suka tsere, amma duk da haka sun tafi da mata huɗu.
Sai dai ya bayyana cewa akwai wani malamin makaranta, Mustafa Malam Malam, da aka taɓa yin garkuwa da shi a baya.
Duk da cewa an biya kudin fansar Naira miliyan ɗaya da rabi, ba su sake shi ba, daga baya suka kashe shi.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Sabon Birni, Alhaji Ayuba Hashimu, ya musanta batun cewa an kai hari masallaci.
Ya ce babu masallacin da aka kai wa hari ko aka kashe limami kamar yadda ake yaɗawa a kafofin watsa labarai.
Shi ma ɗan majalisar yankin, Aminu Boza, ya ce ba su da labarin wani hari da aka kai wa masallaci a yankin.
A wani labarin kuma, ’yan bindiga sun kai hari ƙauyen Shallah da ke mazabar Turba a Ƙaramar Hukumar Isa, inda suka kashe mutum ɗaya.
Daga nan sai suka wuce garin Barkeji, inda suka ƙone rumbunan abinci a daren ranar Asabar.
Ya zuwa yanzu babu wata sanarwar daga rundunar ’yan sandan jihar.