Ya ƙara da cewa Kaduna ita ce jihar da ta cika ƙa’idojin da aka shimfiɗa a yarjejeniyar Malabo kan saka hannun jari a harkar noma.

Shugaban AUDA–NEPAD a Nijeriya, Honarabul Jabir Abdullahi Tsauni, ya yaba wa gwamnatin Jihar Kaduna bisa samar da kuɗaɗen haɗin gwiwa da suka bai wa shirin damar faɗaɗa zuwa dukkan ƙananan hukumomi 23 na jihar.

A cewar Tsauni, an horar da ƙanana manoma 345 kan kyawawan hanyoyin noma da kuma dabarun noma masu jituwa da yanayin sauyin yanayi, ciki har da noman lambu na gida irin su tumatir, barkono mai zaƙi, masara, wake, da waken soya.

Komashinan noma na Jihar Kaduna, Murtala Dabo, ya bayyana cewa wannan shiri ya nuna yadda Kaduna ke da niyyar mayar da noma a matsayin sana’ar da ke kawo riba, ba kawai hanyar rayuwa ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru October 26, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL October 26, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu October 26, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamishinan Gombe ya rasu a hatsarin mota

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Gombe, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), ya rasu a hatsarin mota.

Gwamnatin Jihar Gombe ce, ta sanar da rasuwar cikin wata sanarwa da Daraktan Harkokin Watsa Labarai, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a ranar Juma’a.

Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC Gwamnan Bauchi ya naɗa ɗan uwansa a matsayin sabon Sarkin Duguri

Sanarwar ta ruwaito cewa Bello ya rasu a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe, bayan aukuwar wani mummunan hatsarin mota.

“Gwamnatin Jihar Gombe na cikin jimamin sanar da rasuwar Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), sakamakon a hatsarin mota da ya rutsa da shi a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe,” in ji Misilli.

Sanarwar, ta bayyana cewa Bello ya rasu tare da wani jami’in ɗan sanda da ke tare da, Sajan Adamu Husaini.

Hatsarin ya rutsa da su yayin da suke dawowa daga Maiduguri, Jihar Borno, inda suka halarci wani taro na yankin Arewa Maso Gabas.

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana labarin rasuwar Kwamishinan a matsayin abun baƙin ciki.

Ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai biyayya, jajircewa da yi wa jama’a hidima, wanda ya nuna ƙwarewa wajen jagoranci da kishin ƙasa a ayyukansa a Gombe.

“Kanal Bello (mai ritaya) zai kasance abin koyi wajen biyayya, hidima ba tare da son kai ba.

“Ya gudanar da aikinsa da himma. Rashinsa babban giɓi ne ba wai ga iyalansa da gwamnatinmu ba, har ma da Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya,” in ji gwamnan.

Gwamnan ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, abokan aikinsa, da al’ummar Ƙaramar Hukumar Balanga.

Hakazalika, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan jami’in ɗan sandan da ya rasu tare da Kwamishinan.

Ya yi addu’ar Allah Ya gafarta musu tare da sanya su a Aljanna Firdausi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
  • An ba da tallafin N2m ga iyalan jami’in NSCDC da aka kashe a Jigawa 
  • Kwamishinan Gombe ya rasu a hatsarin mota
  • Shirin Soil Values Da NAIDA Sun Fito Da Tsarin Saukaka Samun Kayayyakin Gona Ga Manoma
  • Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
  • Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata
  • Gwamnatin Jihar Sokoto Ta Amince da Sauya Amfani da Naira Biliyan 526 a Kasafin Kuɗin 2025
  • Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
  • Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba