Gwamnatin Kaduna Tare Da AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma
Published: 26th, October 2025 GMT
Ya ƙara da cewa Kaduna ita ce jihar da ta cika ƙa’idojin da aka shimfiɗa a yarjejeniyar Malabo kan saka hannun jari a harkar noma.
Shugaban AUDA–NEPAD a Nijeriya, Honarabul Jabir Abdullahi Tsauni, ya yaba wa gwamnatin Jihar Kaduna bisa samar da kuɗaɗen haɗin gwiwa da suka bai wa shirin damar faɗaɗa zuwa dukkan ƙananan hukumomi 23 na jihar.
A cewar Tsauni, an horar da ƙanana manoma 345 kan kyawawan hanyoyin noma da kuma dabarun noma masu jituwa da yanayin sauyin yanayi, ciki har da noman lambu na gida irin su tumatir, barkono mai zaƙi, masara, wake, da waken soya.
Komashinan noma na Jihar Kaduna, Murtala Dabo, ya bayyana cewa wannan shiri ya nuna yadda Kaduna ke da niyyar mayar da noma a matsayin sana’ar da ke kawo riba, ba kawai hanyar rayuwa ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Kwamishinan Gombe ya rasu a hatsarin mota
Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Gombe, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), ya rasu a hatsarin mota.
Gwamnatin Jihar Gombe ce, ta sanar da rasuwar cikin wata sanarwa da Daraktan Harkokin Watsa Labarai, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a ranar Juma’a.
Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC Gwamnan Bauchi ya naɗa ɗan uwansa a matsayin sabon Sarkin DuguriSanarwar ta ruwaito cewa Bello ya rasu a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe, bayan aukuwar wani mummunan hatsarin mota.
“Gwamnatin Jihar Gombe na cikin jimamin sanar da rasuwar Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), sakamakon a hatsarin mota da ya rutsa da shi a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe,” in ji Misilli.
Sanarwar, ta bayyana cewa Bello ya rasu tare da wani jami’in ɗan sanda da ke tare da, Sajan Adamu Husaini.
Hatsarin ya rutsa da su yayin da suke dawowa daga Maiduguri, Jihar Borno, inda suka halarci wani taro na yankin Arewa Maso Gabas.
Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana labarin rasuwar Kwamishinan a matsayin abun baƙin ciki.
Ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai biyayya, jajircewa da yi wa jama’a hidima, wanda ya nuna ƙwarewa wajen jagoranci da kishin ƙasa a ayyukansa a Gombe.
“Kanal Bello (mai ritaya) zai kasance abin koyi wajen biyayya, hidima ba tare da son kai ba.
“Ya gudanar da aikinsa da himma. Rashinsa babban giɓi ne ba wai ga iyalansa da gwamnatinmu ba, har ma da Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya,” in ji gwamnan.
Gwamnan ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, abokan aikinsa, da al’ummar Ƙaramar Hukumar Balanga.
Hakazalika, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan jami’in ɗan sandan da ya rasu tare da Kwamishinan.
Ya yi addu’ar Allah Ya gafarta musu tare da sanya su a Aljanna Firdausi.